Ƙaramin ministan ilimi a Najeriya Dakta Yusuf Sununu ya ce gwamnatin tarayya ba ta hana dalibai yan ƙasa da shekara 18 rubuta jarrabawa ba.

 

Ministan ya ce gwamnatin ba ta hana dalibai rubuta jarrabawar kammala sakadire ba

 

Dakta Sununu ya bayyana haka ne yau yayin wani taro a Abuja.

 

A cewarsa, mutane basu fahimci bayanin ministan ilimi Farfesa Tahir Mamman ba.

 

Ya ce sun kadu da su ka samu labarin cewar ana baiwa dalibai yan shakara 10, 11 da 12 gurbin karatu a manyan makarantu.

 

Duk da cewar akwai yan baiwa da za su iya kararu a manyan makarantun, sai dai ya c ba su da yawa.

 

Dakta Sununu ya ce gwamnati ba ta hana ɗalibai ƴan ƙasa da shekara 18 rubuta jarrabawar WAEC da NECO a ƙasar ba

 

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya an kai ruwa rana kan bai wa dalibai yan ƙasa da shekara 18 gurbin karatu a jami’a da sauran manyan makarantu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: