Gwamnatin jihar Kano ta soke komawar ɗalibai makaranta ranar Litinin.

 

Hakan na kunshe a wani sakon murya da kwamishinan ilimi a jihar Umar Haruna Doguwa ya sanar.

 

Ya ce an dakatar da komawa makarantar ne saboda wasu abubuwa dasu ka taso.

 

Sannan ya ce za a sanar da ranar komawa nan gaba kaɗan.

 

Kwamishinan ya bai wa iyaye hakuri dangane da jinkirin da aka samu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: