Gwamnatin jihar Kano ta soke komawar ɗalibai makaranta ranar Litinin.

Hakan na kunshe a wani sakon murya da kwamishinan ilimi a jihar Umar Haruna Doguwa ya sanar.


Ya ce an dakatar da komawa makarantar ne saboda wasu abubuwa dasu ka taso.
Sannan ya ce za a sanar da ranar komawa nan gaba kaɗan.
Kwamishinan ya bai wa iyaye hakuri dangane da jinkirin da aka samu.