Rundunar sojin sama a Najeriya ta ce ta fara bincike a kan zargin harin bam da aka jefawa masallata a jihar Kaduna.

 

Daraktan yaɗa labarai na rundunar Kabiru Ali ne ya shaida haka a wata sanarwar da ya fitar yau Litinin.

 

Sai dai ya sake musanta zargin wanda ya ce harin da aka kai kan ƴan bindiga ne kuma ba a kai wa masallata ba.

 

Ana zargin jami’an sojin saman Najeriya da jefa bam kan masallata a ƙauyen Jika da akilo da ke yankin Yadin Kidandan a karamar hukumar Giwa ta jihar.

 

Kusan mutane 25 ake zargi sun rasa ransu wanda daga ciki akwai yara ƙanana.

 

A ɓangaren jami’an kuwa sun musanta kai wa masallatan hari yayin da su ke tsaka da salla a ranar Juma’a.

Leave a Reply

%d bloggers like this: