Jam’iyyar APC a Najeriya ta ce shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba zai jingine kudirin da ya dauka na gyaran kasa tare da komawa baya ba.

A cewar jam’iyyar matakin da shugaban ke ɗauka hanya ce don kawo sauyi da cigaba ga ƙasar.

Sannan jam’iyyar ta musanta zargin yin magudi a yayin zaben da aka yi a Jihar Edo.

A sakon da jam’iyyar APC ta fitar a yau wnda ke zama martani ga jam’iyyar PDP, daraktan yada labarai na jam’iyyar Alhaji Bala Ibrahim ya ce jam’iyyar ba ta da nufin sauka daga turbar demokaradiyya.

Ya ce tsari da manufofin da jam’iyyar ta saka a gaba asara ce kuma ci gaba ne ga ƙasar.

Haka kuma tsarin da su ke kai ba zai tauye demokaradiyya ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: