Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayyana yadda ya ke magana da Shugaba Tinubu kan matsalar tsaron jihar.

 

Uba Sani ya ce a kullum ya na magana da Tinubu akalla sau biyu domin ganin an shawo kan matsalar tsaron a jihar.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin hira da gidan talabijin na Channels a birnin Abuja.

 

Ya bayyana cewa shugaba Tinubu da hafsoshin tsaro sun himmatu wurin tabbatar da kawo karshen matsalar tsaro a kasar.

 

Ya ce ya yi amanna da irin himmatuwar Tinubu wurin dakile matsalar tsaro ganin yadda ya ke nuna damuwa.

 

Ana ci gaba da samun rahotannin garkuwa da mutane da kashe-kashe wanda ya ƙara ta’azzara a kwanakin nan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: