Wasu da ake zargi yan bindiga ne sun kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu da dama a jihar Zamfara.

 

Harin da su ka kai a jiya da daddare, sun lalata karfen sadarwa na kayin waya wanda hakan ya hana damar sadarwar a garin.

 

Yaan bindigan sun kai hari garin Dauran a ƙaramar hukumar Zurmi ta jihar

 

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Yazid Abubakar ya tabbatar da faruwar hakan yau Alhamis.

 

Ya ce mutane uku aka kashe a garin yayin da aka yi garkuwa da wani mutum guda.

 

Sannan sun kone wata tashar sadarwar layin kira na MTN a garin.

 

Ƴan bindigan sun shiga garin dauke da muggan makamai.

 

Mazauna garin sun shaida cewar an kashe mutane uku sannan an yi garkuwa da wasu mutane da ba a kai ga ganosu yawansu ba a masarautar Zurmi.

 

A garin na Dauran kuwa, an yi garkuwa da mutane biyar

 

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: