Babbar kotun tarayya da ke jihar   Kano karkashin mai shari’a Lures    Okapo ta zauna don sauraron shaidu dangane da zargin ɗan takarar gwamnan kano Abdussalam            Abdulkarin AA Zaura.

Hukumar yaki da masu yiwa ƙasa zagon ƙasa EFCC ta gurfanar da AA Zaura ne bisa zargin damfarar wani Balarabe maƙudan kuɗade.

Kotun wadda ta saka ranar 29 ga watan Janairun 2019 don gabatar da shaidu, alƙalin kotun ya zauna tdon yin shairi’ar amma ɓangaren masu ƙara ba su samu damar halartar kotun ba.

Hakan ya sa aka ɗage zaman kotun zuwa 1 da 2 da 3 ga watan Afrilun 2019.

Mahaifin tsohon Gwamnan Kano    kuma hakimin Madobi Alhaji Musa Saleh Kwankwaso ya nuna         Gwamnnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin wanda ya cancanta a zaɓa a zaben 2019 kamar yadda sakataren yaɗa labaran    gwamnan ya wallafa.

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: