Connect with us

Labaran ƙasa

Hukumar EFCC na fuskantar Matsala Wajen Dawo Da Kudaden da Aka Boye A Kasashen Waje

Published

on

Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC Ibrahim Magu ya koka kan yadda suke wahala wajen dawo da Kudaden da aka boye a Kasashen waje Wanda wasu shuwagabannin suka boye.

Magu ya kuma yi Roko ga hukumomi da suke da Ruwa da tsaki na duniya dasu taimakawa hukumar akan hanyoyin da za’abi wajen dawo da Kudaden gida Najeriya.

Cikin wata sanarwa da kakakin Hukumar Mista Tony Orilade ya fitar a jiya cewa na cikin damuwa kan Rashin dawo da Kudaden.

A cewar Magu hanyoyin da ake bi wajen dawo da Kudaden da aka boye su a Kasashen waje suna da Wahala matuka.
Wannan yasa dole su nemi sabbin dabaru wajen ganin An dawo da Kudaden.

Click to comment

Leave a Reply

Labaran ƙasa

Mutane Sama Da 7,000 Sun Dawo Najeriya Bayan Tserewa Sakamakon Rikicin Boko Haram

Published

on

Gwamnatin tarayya a Najeriya ta dawo da mutane 7,790 waɗanda su ka yi gudun hijira sakamakon hare-haren mayakan Boko Haram.

Hadimin gwamnan jihar Borno Dauda Iliya ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar yau a Maiduguri

Ya ce gwamnan jihar Babagana Zulum ne ya jagiranci tawagar gwamnatin tarayya don dawo da mutanen da su ka yi hijira zuwa Najeriya.

Sanarwar ta ce an dawo da mutanen ne daga ƙasar Chadi.

Ministan jin kai. Najeriya Dakta Yusuf Sununu na daga cikin waɗanda su ka je wajen

Sai ministan rage talauci Aliyu Ahmed da babban sakatare a hukumar kula da yan gudun hijira

Rahotanni sun ce mafi yawa daga cikin waɗanda su ka yi gudun hijirar ƴan jihar Borno ne.

A cewar gwamna Zulum, waɗanda aka dawo da su iya wadanda au ja nuna sha’awar dawowa ne.

Gwamnatin tarayya ta nuna jin daɗi bisa yadda ƙasar Chadi ta rungumi yan kasar tsawon shekaru.

Continue Reading

Labaran ƙasa

Ƙarin Kuɗin Kira Da Na Data Zai Kai Kaso 30 Zuwa 60 A Najeriya

Published

on

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce akwai yiwuwar ƙara kudin kiran waya da data da aika sakonni da kaso 30 zuwa 60.

Ministan sadarwa na ƙasa Dakta Bosun Tijani ne ya bayyana haka yayin wata ganawa da aka yi da shi a gidan talabiji na Channels.

Ministan ya ce sun karbi rahoto daga masu masana masu zaman kansu kan yadda karin zai kasance

Tun tuni ministan ya yi watsi da bukatar kara kudin da kaso 100 wanda kamfanonin sadarwa su ka bukata.

A cewarsa, za a yi karin kuma ba da jimawa ba amma ba zai kai da kaso 100 ba.

A makon da ya gabata aka fara wani zama da masu ruwa da tsaki kan batun, kuma aka bayar da umarnin nazartar buƙatar haka.

Kamfanonin sadarwa a Najeriya ne dai su ka ce ba za su iya ci gaba da gudanar da ayyukansu ba na tare da sun yi ƙari a kan kudaden kira da data da kuma na aika sakonni ba.

A cewarsu matukar ana buƙatar ingantaccen sadarwa a ƙasa to ya zama wajibi a yi karin kuɗaɗen.

Continue Reading

Labaran ƙasa

Babu Ranar Gyara Wutar Lantarkin Arewa – Gwamnatin Tarayya

Published

on

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce babu ranar daina lalacewar wutar lantarki musamman babban layin da ke kai wuta yankin arewa.

Ministan makamashi Adebayo Adelabu ne ya bayyana haka yayin kare kasafin kudi na shekarar 2025 a gaban kwamitin majalisar dokoki kan makamashi.

Adebayo ya ce sakamakon rashin tsaro ya sa gwamnatin tarayya ba za ta iya tabbatar da ranar daina lalacewar wutar yankin arewa da kuma gyarawa ba.

A cewarsa, babban layin Kaduna zuwa Shiroro zu a Mando shi ne layi na biyu mafi girma da ke kai wutar lantarki arewa, kuma har yanzu ba a gyara ba saboda rashin tsaro.

A sakamakon rashin gyaran ne ya sa sauran layikan ke ci gaba da faduwa.

Ya ce a yanzu za a ci gaba da fuskantar yawan faduwar layukan wutar.

Ministan ya ce hadin gwiwar da su ka yi da ofishin mashawarcin shugaban kasa kan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribadu bai kawo karshen kalubalen da bangaren ke fuskanta ba.

Ministan ya ce su na shirin saka kyamarorin tsaro da fitilu masu amfani da hasken rana a wuraren da hanyoyin layin lantarki ya ketara domin magance matsalar a gaba.

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: