Connect with us

Labarai

Har yanzu an kasa kawo Karshen Talauci a Najeriya– ATIKU

Published

on

Tsohon mataimakin shugaban kasar najeriya kuma Dan takarar shugabancin kasar nan a inuwar jami’ar PDP Atiku Abubakar shine ya bayyana hakan.

Inda ya ce Nijeriya tana shiga matsanancin talauci, ga cin hanci da kuma kin gaskiya duk a karkashin mulkin Shugaba Muhammadu Buhari.

Wannan furuci ya fito ne ta Bakin mai taimakawa Atikun akan kafafen yada labarai Mr Paul Ibe ta cikin wata takarda da ya fitar aka rabawa manema labarai a yau
inda yace yan Nijeriya suna rayuwa cikin matsanancin talauci tun daga ranar da Buhari ya zama shugaban kasa a shekarar 2015 har zuwa yau.
Atiku ya ce rahoton Majalisar Dinkin Duniya ne ya kara fadakar da ‘yan Nijeriya kan irin gararin da suke ciki saboda yadda gwamnatin Buhari ta nuna gazawa wurin gyara tattalin arzikin kasar.
Rahoton ya bayyana cewa akwai ‘yan Nijeriya miliyan 98 da ke rayuwa cikin matsanancin talauci. ya kuma nuna mamakinsa matuka kan yadda gwamnatin Buhari ta yi na nuna rashin damuwa da wannan rahoto na majalisar dinkin duniya ta fitar.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

An Kone Ofishin Yan Sanda A Anambra

Published

on

Wasu ƴan daga sun kai hari tare da ƙone ofishin ƴan sanda a jihar Anambra.

 

An kai harin ne ofishin ƴan sanda na Neni da ke ƙaramar hukumar Anaocha a jihar da misalin ƙarfe 02:00am na dare wayewar yau Alhamis.

 

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Tochukwu Ikenga ya ce mutanen sun kai harin ne da abin fashewa da ake zargi bam ne.

 

Sannan ya ce maharan ba su ɗauki makaman jami’an ko yin garkuwa da jami’an su ba.

 

Ya ƙara da cewa, maharan sun gudu bayan da ƴan sanda su ka ci ƙarfinsu.

 

Zuwa yanzu ana ci gaba da hibiya don gano su waye su ka kai harin tare da kamasu.

 

Sai dai bai bayyana asarar da aka yi ba a sakamakon harin da aka kai.

 

 

Continue Reading

Labarai

An Kama Ƴan Fashin Da Su Ka Yi Wa Matar Aure Fyaɗe A Jigawa

Published

on

Rundunar ƴan sanda a jihar Jigawa sun kama wasu mutane uku da ake zargi da aikata fashi da makami haɗi da fyaɗe ga matar aure a jihar.

 

Kwamishinan ƴan sandan jihar AT Abdullahi ne ya bayyana haka yau Alhamis.

 

Ya ce an kama mutane uku bayan da su ka shiga gidan wani Mudan Ibrahim mazaunin ƙauyen Chori a ƙaramar hukumar Ringim tare da yi masa fashi daga bisani su ka yi wa matarsa fyaɗe.

 

Ƴan sandan sun samu labarin ne a ranar 17/03/2024.

 

Bayan zurfafa bincike, jami’an sun kama wani Umar Ibrahim, Umar Nasara, da wani Abubakar Isah dukkaninsu mazauna ƙauyen Chori a jihar.

 

Tuni aka ci gaba da zurfafa bincike a kai, kuma da zarar an kammala za su gurfanar da su a gaban kotu kamar yadda kwamishinan ya shaida.

 

A wani labarin kuma kwamishinan ya bayyana nasarar kama wasu ƴan fashi da makami, da kuma wasu da ake zargi da aikata sata a jihar.

 

 

Continue Reading

Labarai

Malamin Makaramtar Firamare Na Kuriga Ya Mutu A Hannun Ƴan Bindiga Kafin Kuɓutar Da Dalibai

Published

on

Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya sha alwashin ɗaukar nauyin karatun ɗalibai 137 da aka kuɓutar daga hannun ƴan bindiga.

 

Ɗaliban su ne waɗanda aka yi garkuwa da ssu daga makarantar firamare ta Kuriga a jihar.

 

Gwamnan ya ce zai ɗauki nauyin karatun nasu ne daga matakin Firamare zuwa sakandire ƙarƙashin cibiyar Uba Sani Foundation.

 

Gwamnan ya bayyana haka yau Alhamis kafin mayar da ɗaliban zuwa Kuriga.

 

Ya ce bayan kuɓutar da su, an ɗauki lokaci domin duba lafiyarsu kafin miƙasu ga iyayensu.

 

Ya ce guda cikin malaman da aka yi garkuwa da su mai suna Malam Abubakar, ya rasa ransa a hannun ƴan bindigan.

 

A sakamakin haka, gwamnan ya ce zai ɗauki nauyin karatun ƴaƴan malamin, tare da bai wa iyalansa naira miliyan goma.

 

Akwai waɗanda su ka samu larurar kwakwalwa daga cikin ɗaliban da aka kuɓutar, a don haka su ka miƙasu ga kwararrun likitoci domin duba lafiyarsu.

 

Sannan gwamnatin ta bayar da umarnin yin wasu ayyuka a Kuriga, wamda gwamnan ya ce garin na daga cikin garuruwan da su ka fi zaman lafiya a jihar.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: