Connect with us

Labarai

Zaɓe a Kano – Rundunar ƴan sanda ta haramta zirga-zirga a ranar Asabar mai zuwa

Published

on

 

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano karkashin jagorancin Kwamishinanta *Cp Habu A. Sani, psc* na sanar da al’ummar Jihar kano cewa, *Hukumar zabe mai zaman kanta wato INEC zata sake gudanar da zabuka Ranar Asabar 25/01/2020 a Kananan hukumomin Bebeji, Tudun Wada, Doguwa, Rogo, Kumbotso, Kiru, Bunkure, Minjibir da kuma Karamar Hukumar Madobi.*

Hukumar na bada tabbacin cewa *tayi hadin kai da takwarorin hukumomin tsaro dake nan Kano domin tabbatar da anyi zabe lafiya an kuma gama lafiya*,

A don haka, al’umma su tabbata sun kiyaye da:-

1. Duk wani motsin ababen hawa kamar Motoci, Adaidaita Sahu da Babura an haramta shi tun daga daren jajiberen ranar zaben har a kammala a wadannan kananan Hukumomi Guda Tara da za’ayi zabe, in banda motocin Asibiti, Jami’an Kashe Gobara, Ma’aikatan zabe da wadanda hukumar zaben ta tantance.

2. Ba’a yarda duk wasu matasa yan tada zaune tsaye su kusanci inda ake gudanar da zaben ba.

3. Daukar duk wani makami ko kuma abun cutarwa a yayin gudanar da zaben, jami’an tsaro ba za su amince da haka ba.

4. Iya wadanda suka cancanci zabe za’a bari a harabar zaben.

5. Duk wanda bashi da katin zabe da yake nuna lambar akwatin zabensa a wannan yanki, hukuma zatayi awon gaba dashi.

6. Bamu aminta da kawo wani mutum ko wasu mutane inda ake zaben ba. Matukar ba hukumar INEC ce ta tantance suba sannan iya wakilan Jam’iyyun da hukumar zabe ta tantance aka amince da zuwan su zaben.

7. Rundunar ‘Yan sanda ta Jihar Kano na yiwa al’umma fatan yin zabe lafiya kuma a gama lafiya.

Don neman taimakon gaggawa ko kuma sanar da faruwar wani lamari, sai a kira wadannan lambobin *08032419754, 09029292926, 08123821575*.

*Mungode da hadin kan da ake bamu*

*MAI SANARWA*
DSP ABDULLAHI HARUNA
KAKAKIN RUNDUNAR ‘YAN SANDAN JIHAR KANO
*AMADADIN KWAMISHINAN ‘YAN SANDAN JIHAR KANO*

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Sheikh Ahmad Gumi Yayi Allah Wadai Da Kashe Al’umma Masu Taron Maulidi A Kaduna

Published

on

Fitaccen malamin addinin musulunci a Najeriya Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya yi Allah-wadai da hallaka mutane da jirgin soji yi a garin Tudun Biri a Jihar Kaduna.

Malamin ya bayyana hakan ne ta cikin wani jawabi da ya fitar a shafinsa na Facebook, Gumi ya ce lamarin abin takaici ne da ke yawan faruwa a yankin Arewacin Kasar.

Sheikh Ahmad Gumi ya kara da cewa ana maida Jihohin Arewacin Kasar tamkar zirin Gaza, kamar yadda sojojin Israila su ke hallaka mutanen kasar Falasdin.

A jawabin na Gumi ya zargi hukumomin Kasar da nufi mara kyau ga mutanen Kasar, tare da yin kisan kare dangi da ganganci ga al’ummar da ke kauyukan Arewa.

Gumi ya ce hakan ba zata taba yuwuwa ba jirgin yayi kuskure wajen sanya bam ga masu fararen kaya ba.

Ahmad Abubakar Gumi ya bayyana cewa akwai wata a kasa wajen sanyawa masu taron mauludin bom din da jirgin yayi.

Continue Reading

Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayarwa Da Peter Obi Martani Akan Sukar Shugaba Tinubu

Published

on

Fadar shugaban kasa ta yiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party ga Peter Obi raddi akan yadda ya ke sukar gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Martanin ya fito ne daga ofishin Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ta bakin mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha a ranar Talata.

Sanarwar ta zargi Peter Obi da bata gwamnatin Tinubu bisa rashin nasarar da ya samu a lokacin zaben kasar.

Sanarwar ta ce Peter ya yi amfani da zargin zuwa taron COP na 28 da shugaban ya tafi da mutane 1411, domin cimma wata manufa tasa ta siyasa ta hanyar yaudara.

Sanarwar ta ce Obi ya shafe tsawon lokaci ya na sukar gwamnatin ta Tinubu domin ya nuna cewa ya na kishin kasa, kuma ba gaskiya yake fada ba a kalamannasa.

Martanin na zuwa ne bayan da Peter Obi ya soki gwamnatin tarayya akan kudin da aka kashe wajen zuwa taron dumamar yanayi na COP karo na 28 da kuma shirin gyara gidan mataimakin shugaban kasar Kashim Shettima.

 

Continue Reading

Labarai

Kar Gwamnatin Tarayya Ta Fara Tunanin Yafe Kisan Da Sojoji Suka Yiwa Mutane A Kaduna – Sheikh Yahaya Jingir

Published

on

Shugaban Majalisar Malamai na Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa’ikamatis Sunnah ta Kasa, Sheikh Muhammad Sani Yahya Jingir, ya bayyana cewa kada gwamnatin kasar ta fara batun cewa a yafe kisan da sojoji suka yi wa mutane a gurin taron Mauludi a Jihar Kaduna, domin Allah ya yi umarnin a hukumta dukkan wanda ya aikata irin haka.

Sheikh Yahya Jingir ya bayyana hakan ne yayin wani taron ganawa da manema labarai da ya yi a gidansa da ke garin Jos.

Jingir ya ce kisan gilla da aka yiwa mutanen abu ne wanda ba za a taba lamunta ba, kuma ba za a barshi haka ba, ba tare da an hukumta wadanda suka aikata aika-aika ba.

Shugaban ya kara da cewa dole ne a hukumta dukkan wanda aka samu da hanu akan lamarin,kisan mutanen da basuji ba su gani ba,kuma hakkin kowanne shugaba ne ya kare rayukan al’ummar da ya ke jagoranta.

Jirgin ya ce hukunta wadanda suka kashe mutanen da basuji ba su gani ba shine kyakkyawan shugabanci ga kowanne irin shugaba.

Ya ce Allah Ya haramta kisan bayin Allah, ko Musulmi ne ko Kirista ne ko wanda ba shi da addini ne, domin yana da daraja da ’yancin rayuwa, a wajen Allah.

Malamin ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta kafa kwararran Kwamitin bincike, wanda zai binciko musabbabin hallaka mutane.

Malamin ya yi kira da jami’an sojin da sauran hukumoomin tsaro a Kasar,da su dunga tsara yadda za su gudanar da ayyukansu kafin yi,domin kaucewa aikata ba dai-dai ba.

Daga karshe Malaman Jingir ya mika sakon ta’aziyarsa ga Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na lll da Sarkin Zazzau da gwamnan Jihar ta Kaduna da kuma ‘yan uwa da iyalan wadanda suka rasa rayukansu a hari.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: