Mai dakin gwamnan jihar kaduna Hajiya  Aisha El’Rufa’I , tayi kira da a ringa fallasa masu aikata laifin fyaɗe .

Hajiya Aisha tayi wannan kiran ne yayin wani gangami  data jagoranta a kaduna sannan ta hori masu unguwanni da dagatai  da su daina rufa asirin masu aikata laifin.

Haka kuma tace a ringa tabbatarwa ana hukunta duk wanda aka samu da cin zarafi   musamman  laifin aikata fyade.

Matsalar fyade tayi tsamari a najeriya  cikin wannan shekara  wanda hakan ke jawo wasu daga cikin  wanda akaiwa fyade rasa rayukansu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: