Ma’aikatar hajji da umara a ƙasar saudiyya ta saka doka a kan maus shiga masallacin makkah da madina.
![](https://matashiya.com/wp-content/uploads/2020/12/mn-1.jpg)
Ma’aikatar ta ce babu wanda zai shiga ,masallacin har sai an tabbatar an yi masa rigakafin cutar Korona.
A cikin shirye-shiryen tinkarar ibada a watan azumi, ma’aikatar ta samar da wata manhaja musamman domin tantance mutanen da aka yi wa rigakafin cutar.
![](https://matashiya.com/wp-content/uploads/2021/10/DSC_9894-scaled.jpg)
Daga cikin dokokin an haramta wa yara shiga ko kusantar masallatan makkah da madina.
![](https://matashiya.com/wp-content/uploads/2020/02/matashiya-photo-2.jpg)
Haka kuma an taƙaita lokutan sallan tuhajjud da tarawih wanda aka ƙayyade mintuna talatin kacal a sallolin biyu a dukkanin masallatan.
Sai kuma tarar riyal dubu goma ga duk wanda ya karya ƙa’idar da aka shimfida wajen gudanar da ibada a masallacin, haka kuma ga duk wanda ya shiga masallacin ba tare da izni ba zai biya tarar riyal dubu ɗaya.
Ko a baya sai da yariman saudiyya salman ya bayar da umarnin rage raka’o’in sallar tuhajjud da tarawih domin kaucewa yaduwar cutar Korona.
A na sa ran za a fara gudanar da azumi a bata daga gobe Talata.