Ministan babban birnin tarayya Abuja Muhammad Bello ya bayar da umarnin taƙaita mutane yayin gudanar da sallar idi a Abuja.
![](https://matashiya.com/wp-content/uploads/2020/12/mn-1.jpg)
Ministan ya dakatar da gudanar da idin ƙaramar sallar a babban masallacin idi na ƙas da ke babban hanyar Umaru Musa Ƴa’adua a Abuja.
A cikin wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaran minitan Mista Anthony Ogunlaye ya fitar, ya ce an umarci mutane a su gudanar da sallar idin su a masallatan juma’a mafi kusa da su.
![](https://matashiya.com/wp-content/uploads/2021/10/DSC_9894-scaled.jpg)
An yanke hukuncin hakan ne bayan wani zama tsakanin mistan da wakilan malamai a Abuja.
![](https://matashiya.com/wp-content/uploads/2020/02/matashiya-photo-2.jpg)
Umarnin yin sallar idi a masallatan juma’a wanda aka ce kada a haura mutane hamsin a masallaci.
Sanarwar ta umarci mazuna Abuja da su gudanar da shagulgulan sallar su a gidajen su, yayin da ak abayar da umarnin rufe dukkanin gidajen wasa, da sauran wuraren shaƙatawa.
Dukkan wannan mataki ya biyo bayan saka sabuwar dokar kulle da aka yi a Najeriya domin rage yaɗuwar cutar Korona.