Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu ya amince a cire kashi 3% na albashin ma’aikatan gwamnatin jiharsa a karkashin shirin inshoran lafiya na Kebbi State (KECHEMA).

Wannan batu na amincewar gwamnan na zuwa ne daga bakin mai ba shi shawari kan harkokin yada labarai, Malam Yahaya Sarki a yau Talata a birnin Kebbi.

Alhaji Safiyanu Garba-Bena, mukaddashin shugaban ayyuka na jihar ya ce, amincewar gwamnan ya biyo bayan bukatar da kungiyar kwadago ta gabatar a jihar.

A tun farko, kungiyar ta kwadago ta nemi a cire kasho 3% daga albashin ma’aiakata tare da tura su ga asusun KECHEMA.

A cewar gwamnatin jihar, wannan zaftare albashi zai fara aiki ne daga wannan watan na Nuwamba don turawa ma’aikatar KECHEMA ta fara shirin samar da kayayyakin kiwon lafiya ga ma’aikatan gwamnati.

Leave a Reply

%d bloggers like this: