Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum ya karbi bakuncin daruruwan ’yan kasuwar Monday Market, wadanda iftila’in gobara ya shafa.

 

Yawancin ’yan kasuwar, wadda ita ce mafi girma a Maiduguri, babban birnin jihar, sun rasa shagunansu da kayayyakinsu na biliyoyin Naira a gobarar da ta tashi da gabanin wayewar garin ranar Lahadi.

 

A lokacin da ya karbi bakuncinsu, Zulum ya ya mika musu cekin kudi na Naira biliyan daya su raba a matsayin agajin gaggawa ga wadanda abin ya shafa, har zuwa lokacin da kwamitin bincike zai fitar da sakamakon aikin da aka sa shi.

 

A cikin  jawabinsa ga al’ummar jihar a ranar Lahadi bayan ziyarar gani da ido a kasuwar, Gwamna Zulum  ya  yi alkawarin tallafin Naira biliyan daya.

 

Kasuwar Litinin ta Maiduguri, wadda aka ce ita ce mafi girma a yankin Arewa maso Gabas, daya ta kone kurmus sanadiyar gobarar da ta dauki tsawon wasu sa’o’i.

 

Annobar gobarar ta tashi ne tsakanin karfe 1 na safe zuwa 2 na dare, kuma zuwa yanzu ba a san musabbabin tashinta ba.

 

A lokacin da ya karbi bakuncin ’yan kasuwar a ranar Litinin a Maiduguri, a gidan gwamnati, Zulum ya ce, “Na Sake jajanta muku bisa bala’in gobara da ta mamaye kasuwar Litinin da ke Maiduguri baki daya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: