Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres “ya yi kakkausar suka ga sauyin gwamnati da aka samu a Jamhuriyar Nijar ba bisa ka’ida ba, kamar yadda kakakinsa ya Stephan Dujarric ya bayyana a jiya Laraba.

Hakan na zuwa ne bayan da sojojin Nijar suka sanar da juyin mulki a gidan talabijin na kasar, inda suka ce sun jingine aiki da kundin tsarin mulkin kasar, tare da dakatar da dukkan hukumomi da kuma rufe iyakokin ƙasar.

Mista Guterres ya ce ya damu matuka da tsare Shugaba Mohamed Bazoum kana kuma ya damu da lafiyarsa, in ji kakakinsa Stephane Dujarric a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar tayi kira da a gaggauta kawo karshen duk wasu ayyukan da ke kawo cikas ga tsarin dimokuradiyya a Nijar, da nahiyar Afrika.

 

.

Leave a Reply

%d bloggers like this: