Wani dan majalisa tarayyaa mai wakiltar Ovia a jihar Edo Denis idahosa ya bayyana cewa yakamata a soke majalisar dattawan kasar saboda irin asarar kudaden da gwmnatin ke yi akan su.

Denis ya bayyana haka cikin wata hira da aka yi da shi da kamfanin dillacin labarai na kasa Najeriya NAN.

Ya ce ya na fadin hakane ba don ya na daga cikin majalissar wakilai bane, a a ya yi nazarin yadda Najeriya ta karar da kudade ga majalissar dattawa kuma duba da yadda ake fama da rashin tattalin arziki a kasar.

ya ci gaba da cewa Najeriya na iya kirkirar majalisa ta baidaya wadda za ta dinga gabatar da duk abinda kasa ke bukata.

sannan majalissar wakilai kaso da yawa na aikin majalissa ita ce ta ke yi, yakamata a rushe ta datttawa a bar guda daya duk da cewa sau uku su ke zama a majalisa a duk sati sai a kara ya zaman za ai zaman sau biyar a mako.

ya ce ba dabara ba ce ace ya zamana suna da majalisu guda biyu a kasa gashi ana fama da rashin kayan aiki a matsayin su na yan kasa dole indai ana so a samu ci gaba a rushe majalissar dattawan Najeriya domin rage matsin rayuwa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: