Hukumar kashe gobara ta ƙasa reshen jihar Kano ta ce wasu shaguna sun kone a sakamakon wata gobara da ta kama a kasuwar Rimi.

Al’amarin ya faru a daren ranar Laraba wayewar yau Alhamis.

Mai magnaa da yawun hukumar Saminu Yusif Abdullahi ya ce shaguna goma ne su ka kone a sakamakon gobarar.

Ya ce wani mai suna Magaji Umar ne ya sanar da su tashin gobarar.

Ya ce gobarar ta faru a ɓangaren siyar da tabarmi, gado da kayan katako.

Jami’an kashe gobarar sun bazama don ganin an daƙile haka.

Sai dai shaguna goma sun kone da kaya a ciki.

Ya ce a cikin wurin da su ka kone akwai shaguna shida da rumfuna huɗu.

Hukumar ta gano cewa gobarar ta faru ne sakamakon wutar lantarki.

Leave a Reply

%d bloggers like this: