Tun bayan lokacin da aka kama Nnamdi Kanu daga Kasar Kenya, kungiyar IPOB ta gudanar da zanga-zanga daban-daban da daukar haramtattun matakai ciki har da aiwatar da dokar zama a gida a duk ranakun Litinin har sai an sako Nnamdi Kanu.

 

Masana da dama na ta tofa albarkacin bakinsu a kan tasirin da matakin ya yi musamman a yankin Kudu maso Gabas da ma kasa baki daya.

 

Har ila yau a bangaren Gwamnatin Tarayya, musamman yanzu da aka tabbatar da nadin sabbin manyan hafsoshin tsaro, an fara daukar mataki a kan ‘yan haramtacciyar kungiyar ta IPOB.

 

Sabon salon da IPOB ta zo da shi domin matsin lambar a saki shugabanta tun daga ranar 9 ga Agustan 2021 ta yi tsanani a yankin Kudu maso Gabas, har ta kai ga rabuwar mazauna yankin da wasu ‘yan’uwansu.

 

A halin yanzu Litinin ta zama wani bangare na karshen mako.

 

Bankuna, shaguna, kamfanonin sufuri, coci-coci, makarantu da ofisoshin gwamnati dukkan su a kulle suke kasancewa.

 

Wani masanin tattalin arziki, Dakta Dozie Okeke, ya shaida wa manema labarai cewa, ba za a iya kididdige mummunar tasirin da wannan doka ta zaman gida ta haifar ga tattalin arzikin yankin Kudu maso Gabas ba.

 

A watan da mu ke ciki wata kotu ta bayar da umarnin ga hukumaar tsaro ta DSS da su bai wa Nnamdi Kanu damar ganawa da likitocinsa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: