Gwamnan Jihar Neja Umar Bago ya amince da karin albashin wucin gadi na naira 20,000 ga dukkan ma’aikatan jihar.

 

 

 

Gwamnan ya amince da karin albashin ne a taron majalisar zartarwa na Jihar a yau Laraba.

 

 

 

Gwamnan ya ce za a fara biyan karin albashin ne nan take ba tare da an dauki dogon lokaci ba.

 

 

 

A zaman Majalisar gwamna Bago ya bayyana cewa duba da watan azumi da ake ciki gwamnatinsa za ta raba kayan abinci mota 120 ga mabukata a Jihar.

 

 

 

Sanna gwamnan ya ce za kuma a raba dafaffen abinci a gurare daban-daban na Jihar.

 

 

 

Bago ya kara da cewa sun yi hakan ne domin ragewa mutane Jhar radadin halin da ake ciki.

 

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: