Babban Bankin Najeriya (CBN) ya biya bashin dala biliyan 7 da gwamnan bankin, Yemi Cardoso ya gada bayan shigarsa ofis a shekarar 2023.

 

Daraktar yada labaran bankin, Hakama Sidi Ali ita ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Laraba 21 ga watan Maris.

 

Hakama ta tabbatar da biyan dukkan basukan wanda ake ganin zai iya saka darajar naira ta tashi a kasuwar duniya.

 

Ta ce bankin ya dauki wani kamfanin kula da kudi mai suna Deloitte Consulting da zai tabbatar da biyan bashin ga wadanda suka cancanta kadai.

 

A bangare guda kuwa, gwamnan bankin CBN, Yemi Cardoso ya bayyana amfanin biyan bashin domin ɗaga darajar naira.

 

Wannan mataki na daga cikin tsare-tsaren da gwamnatin Bola Tinubu ke dauka domin tabbatar da inganta darajar naira a kasar.

 

Masana na ganin wannan zai kara inganta tattalin arzikin kasar tare da dakile tashin farashin kayayyaki musamman kayan da ake shigo da su daga waje.

Leave a Reply

%d bloggers like this: