Rundunar sojin saman Najeriya sun samu sanarar tarwaatsa sansanin ƴan bindiga a jihar Zamfara.

 

 

 

Nasarar na zuwa ne a ranar Laraba yayin da sojin su ka kai hari ta sama a kan sansanin ƴan bindiga uku wanda ya yi sanadiyyar lalatasu gaba ɗaya.

 

 

 

Mai magana da yawun rundunar Edward Gabkwet ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai yau a Abuja.

 

 

 

Ya ce sansanin da aka lalata mallaki ne ga rikaƙƙen ɗan bindiga Abdullahi Nasanda a Zurmi, Malam Tukur a Gusau, da wani sansani a ƙaramar hukumar Maradun.

 

 

 

Ya ce bayanan sirri da su ka samu ne ya tabbatar musu da sansanin da mutanen Nasanda ke ɓoye a ciki tare da baburansu.

 

 

 

Haka kuma yayin harin sun hallaka ƴan bindiga da dama.

 

 

 

Jirgin sojin ya kai hari sansanin ƴan bindiga a Kanikawa daa k ƙaramar hukumar Maradun kuma a nan ma ya ƙaddamar da hare-haren a kan ƴan bindigan tare da lalata sansanin baki ɗaya.

 

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: