Gwamnatin tarayya a Najeriya ta dawo da mutane 7,790 waɗanda su ka yi gudun hijira sakamakon hare-haren mayakan Boko Haram.

Hadimin gwamnan jihar Borno Dauda Iliya ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar yau a Maiduguri
Ya ce gwamnan jihar Babagana Zulum ne ya jagiranci tawagar gwamnatin tarayya don dawo da mutanen da su ka yi hijira zuwa Najeriya.

Sanarwar ta ce an dawo da mutanen ne daga ƙasar Chadi.

Ministan jin kai. Najeriya Dakta Yusuf Sununu na daga cikin waɗanda su ka je wajen
Sai ministan rage talauci Aliyu Ahmed da babban sakatare a hukumar kula da yan gudun hijira
Rahotanni sun ce mafi yawa daga cikin waɗanda su ka yi gudun hijirar ƴan jihar Borno ne.
A cewar gwamna Zulum, waɗanda aka dawo da su iya wadanda au ja nuna sha’awar dawowa ne.
Gwamnatin tarayya ta nuna jin daɗi bisa yadda ƙasar Chadi ta rungumi yan kasar tsawon shekaru.