Connect with us

Labarai

Sani Bello ya kamu da cutar Korona

Published

on

Kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Twitter, gwamnan jihar Naija Abubakar Sani Bello ya kamu da cutar Korona.

Bayan samunsa da cutar, gwamnan ya killace kansa kamar yadda gwamnatin jihar ta bayyana.

An yiwa gwamnan gwajin cutar kuma aka tabbatar yana ɗauke da ita kuma nan take ya killace kansa.

Idan ba a manta ba ko da a baya, sai da shugaban kwamitin da gwamnatin tarayya ta kafa don daƙile yaɗuwar cutar ya fitar cewa za a samu hauhawar mutanen da cutar za ta harba cikin makwanni biyu.

Ko da rahotannin da aka fitar a jiya, sai da aka samu ƙarin mutane 300 da cutar ta harba.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Fasinjoji Biyu Sun Mutu Sakamakon Ruftawar Gada A Ebonyi

Published

on

Rundunar ƴan sanda a jihar Ebonyi sun tabbatar da mutuwar wasu fasinjoji biyu sanadin ruftawar wata gada a jihar.

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Joshua Ukandu ne ya tabbatar da haka a Abakaliki yau Litinin.

Ya ce lamarin ya faru da misakin ƙarfe 10:00am na safiyar yau a ƙauyen Mgbabeluzor da ke ƙaramar hukumar Izzi a jihar.

Ya ce tuni aka kai gawar mutanen babban asibitin Iboko sashen ajiye gawarwaki.

Gadar wadda ake gyaranta ta rufta yayin da ma’aikatan ke kusa da ita.

Sannan mutanen biyu sun mutu ne sakamakon munanan rauni da su ka samu.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Edo Ya Amince Da Dubu 70 Matsayin Mafi Karancin Albashi

Published

on

Gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki ya amince da dara biyan ma’aikatan jihar mafi ƙarancin albashi naira 70,000.

Obaseki ya bayyana haka yau Litinin yayin ƙaddamar da gidan ma’aikata.

Ya ce zai fara biyan mafi karancin albashin daga watan Mayu mai kamawa.

Batun ƙarin albashi na daga cikin dalilai da ya sa kungiyoyin kwadago a Najeriya ke yin zanga-zanga wanda su ka buƙaci a ƙarawa ma’aikata a kowanne mataki.

A baya ƙungiyar ta bukaci a mayar da mafi ƙarancin albashin naira 30,000, sai sai sun bukaci ƙari bayan da aka cire tallafin mai a shekarar 2023.

Sai dai wasu gwamnonin sun nuna ƙin amincewa da haka a baya.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Kotu Ta Sanya Ranar Da Za Ta Yankewa Ganduje Hukunci Kan Zargin Rashawa

Published

on

Babbar kotun jihar Kano ta tsayar da ranar yanke hukunci dangane da zargin tsohon gwamnan jihar Abdullahi Ganduje bisa karɓar rashawa.

 

Kotun ƙarƙashin mai shari’a Usman Malam Na’abba, ta tsayar da ranar 16 ga watan Mayu a matsayin ranar da za ta yanke hukuncin bayan sauraron kowanne bangare.

 

An shigar da ƙarar tsohon gwamnan Kano Abdullahi Ganduje da matasar da ɗansa kan zargi takwas wanda ciki akwai cin hanci, karkatar da kudaɗe da sauransu.

 

Baya ga tsohon gwaman, akwai wani kamfani da aka shigar da ƙarar wanda yana daga cikin waɗanda ake ƙara.

 

Gwamnatin Kano ce ta gurfanar da su a gaban kotu, tare da gabatarwa da kotu shaidu 15 a kan zargin da take musu.

 

Bayan sauraron ɓangaren masu ƙara da waɗanda ake ƙara, kotun ta tsayar da ranar 16 ga watan Mayu domin yanke hukunci a kai.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: