Connect with us

Labarai

Ƴan Sanda Sun Cafke Wanda Yake Yi Wa Ƴan Bindiga Safarar Makamai

Published

on

Rundunar ƴan sanda a jihar Kebbi ta kama wani da yake yin safarar makamai ga ƴan binga.

Mai Magana da yawun ƴan sandan jihar DSP Nafi’u Abubakar ne ya bayyana hakan wanda ya ce sun kama wani babban mai garkuwa da mutane a jihar.

Ya ce a ranar 27 ga watan Janairun da ya gabata, sun kama wani mai suna Ibrahim Bulun ɗauke da bindigogi ƙirar gida.

Wanda ake zargin ya amsa cewar yana safarar makamai ne ga ƴan bidigan.

DSP Nafi’u Abubakar ya ce suna ci gaba da bincike a kan waɗanda aka kama, kuma za su gurfanar da su a gaban kotu da zarar sun kammala.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

An Bai Wa Kamfanin Wutar Lantarki Mako Guda Ya Cire Karin Kudin Wutar

Published

on

Ƙungiyar ƴan kasuwa a Najeriya ta bai wa hukumar samar da wuta a Najeriya mako guda da ta janye batun ƙarin wutar lantarki da ta yi.

 

 

 

Shugaban ƙungiyar Fetus Osifo ne ya bayyana haka yau Laraba wanda ya ce sam ƙarin bai dace da ƴan Najeriya ba a wannan lokaci.

 

 

 

Yayin da yake jawabi a yau da ake ranar ma’aikata ta duniya, Fetus Osifo ya buƙaci a mayar da tsohon farashin wutar maimakon karin kusan kashi 300 da aka yi a kwanan nan.

 

 

 

Gwamnatin ta ƙara farashin ne zuwa sama da naira 250 kan kowanne megawatt guda maimakon naira 66 da ake biya a baya.

 

 

 

Rukunin da ke kan tsarin band A ne aka yi wa ƙarin wanda gwamnatin ta ce su na samun wuta tsawon awanni 24 a kowacce rana.

 

 

 

Sai dai maganar ta ci karo da wata magana da ministan makamshi ya yi cewar, ba za a taba samun tsayayyar wuta a Najeriya ba har sai an kashe dala biliyna goma duk shekara tsawon shekara goma.

 

 

 

Haka ma mataimakin shugaban ƙasa Sanata Kashim Shettima ya ce ƙasa da kashi 20 na ƴan kasar ne ke morar lantarki yayi da fiye da rabin ƴan kasar ba sa ta’ammali da ita baki daya.

 

 

Continue Reading

Labarai

Dalibai Biyu Sun Rasa Ransu Bayan Shigar Su Dam Din Danbatta

Published

on

Wasu ɗalibai guda biyu sun rasa ransu a yayin da su ka shiga dam din Danbatta a Kano.

 

 

 

Hukumar kashe gobara a Kano ta tabbatar da mutuwar ɗaliban biyu wanɗanda dukkansu ƴan kasa da shekara 25 ne.

 

 

 

Mai magana da yawun hukumar Saminu Yusif ya ce sun samu kiran waya ne daga wani Kwamared Ibrahim Umar Muhammad wand aya sanar da su cewar ɗaliban uku sun shiga dam ɗin Thomas kuma sun kasa fitowa.

 

 

 

Bayan samar da su jami’an hukumar da ke karamar hukumar Dambatta haɗin gwiwa da masunta su ka yi kokarin ceto mutum guda.

 

 

 

Yayin da biyun aka cetosu da yamma kuma a mace.

 

 

 

Daliban na karatun a kwalejin noma da kiwo da ke Danbatta, kuma tuni aka kai guda dake rage asibiti domin kula da lafiyarsa.

 

 

 

Lamarin ya faru a jiya Talata kamar yadda hukumar ta sanar.

 

 

 

Zuwa yanzu hukumar ta ce ta na ci gaba da bincike domin gano dalilin mutuwar tasu.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

NLC Ta Yi Watsi Da Batun Karin Albashi Da Gwamnatin Tarayya Ta Yi

Published

on

Ƙungiyar kwadago a Najeriya ta yi watsi da batun ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yi na wasu rukuni shida.

 

 

 

Kungiyar ta yi watsi da ƙarin tare da jaddada matsayarsu kan mafi karancin albashi naira 615,000.

 

 

 

A wata tattaunawa da mataimakin babban sakataren Christ Onyeka ya bayyanawa jaridar Daily Trust cewar batun bata lokaci ne kawai.

 

 

 

Sai dai har zuwa daren jiya da gwamnatin ta sanar da ƙarin kungiyar ba ta bayyana gamsuwa a kai ba.

 

 

 

Gwamnatin ta ce ta ƙarawa ma’aikatan albashin ne da kashi 25, da kuma kashi 35 ga wasu rukuni shida na ma’aikatan.

 

 

 

Tun tuni ƙungiyoyin kwadago ke kiraye-kiraye da a ƙara musu albashi ganin yadda cire tallafin man fetur ya taɓa al’amura da dama.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: