Connect with us

Labarai

Mu Na Allah Wadai Da Kisan Matafiya A Sokoto – Buhari

Published

on

A wani sakon ta’aziyya da mai magana da yawunsa Femi Adesina ya fitar ya ce bai ji daɗin yadda lamarin ya kasance ba.

Ya ce wannan al’amari na bukatar gudumawar dukkanin al’umma don magance matsalar.

Shugaban Najeriya Buhari ya ce jami’an tsaro za su ci gaba da aiki tukuru don ganin an magance matsalar tsaaro da ta addabi kasar.

Ƴan bindiga sun kone matafiya da ransu a cikin mota a jihar Sokoto.

An tare matafiyan a kan hanyar su ta tafiya.

Tuni aka yi jana’izar mutanen da su ka mutu a sanadin mummunan harin.

A na zargin mutanen da aka kashe sun kai su 23 kuma daga ciki har da jariri sabuwar haaihuwa.

Matsalar tsaro nna ci gaba da yaɗuwa ƴan bindiga na ci gaba da ƙaddamar da hare-hare dun da bayanan da gwamnati ke cewa ta na samun galaba a kan su.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Dalibai Biyu Sun Rasa Ransu Bayan Shigar Su Dam Din Danbatta

Published

on

Wasu ɗalibai guda biyu sun rasa ransu a yayin da su ka shiga dam din Danbatta a Kano.

 

 

 

Hukumar kashe gobara a Kano ta tabbatar da mutuwar ɗaliban biyu wanɗanda dukkansu ƴan kasa da shekara 25 ne.

 

 

 

Mai magana da yawun hukumar Saminu Yusif ya ce sun samu kiran waya ne daga wani Kwamared Ibrahim Umar Muhammad wand aya sanar da su cewar ɗaliban uku sun shiga dam ɗin Thomas kuma sun kasa fitowa.

 

 

 

Bayan samar da su jami’an hukumar da ke karamar hukumar Dambatta haɗin gwiwa da masunta su ka yi kokarin ceto mutum guda.

 

 

 

Yayin da biyun aka cetosu da yamma kuma a mace.

 

 

 

Daliban na karatun a kwalejin noma da kiwo da ke Danbatta, kuma tuni aka kai guda dake rage asibiti domin kula da lafiyarsa.

 

 

 

Lamarin ya faru a jiya Talata kamar yadda hukumar ta sanar.

 

 

 

Zuwa yanzu hukumar ta ce ta na ci gaba da bincike domin gano dalilin mutuwar tasu.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

NLC Ta Yi Watsi Da Batun Karin Albashi Da Gwamnatin Tarayya Ta Yi

Published

on

Ƙungiyar kwadago a Najeriya ta yi watsi da batun ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yi na wasu rukuni shida.

 

 

 

Kungiyar ta yi watsi da ƙarin tare da jaddada matsayarsu kan mafi karancin albashi naira 615,000.

 

 

 

A wata tattaunawa da mataimakin babban sakataren Christ Onyeka ya bayyanawa jaridar Daily Trust cewar batun bata lokaci ne kawai.

 

 

 

Sai dai har zuwa daren jiya da gwamnatin ta sanar da ƙarin kungiyar ba ta bayyana gamsuwa a kai ba.

 

 

 

Gwamnatin ta ce ta ƙarawa ma’aikatan albashin ne da kashi 25, da kuma kashi 35 ga wasu rukuni shida na ma’aikatan.

 

 

 

Tun tuni ƙungiyoyin kwadago ke kiraye-kiraye da a ƙara musu albashi ganin yadda cire tallafin man fetur ya taɓa al’amura da dama.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Rikicin Da ke Faruwa A Iran Da Isra’il Ne Yasa Karancin Man Fetur A Najeriya

Published

on

Ƙungiyar dilallan man fetur a Najeriya IPMAN ta ce rikicin da ke faruwa a ƙasashen Iran da Isra’ila ne ya yi sanadin ƙarancin man fetur a Najeriya.

 

 

 

Sakataren kungiyar na ƙasa James Tor ne ya bayyana haka yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabiji na Arise dangane da ƙarancin man da ake fuskanta.

 

 

 

Ya ce rikicin da ke tsakanin kasashen biyu ne sila ta ƙarancin da tsadar man da ake fuskanta a kasar.

 

 

 

Kusan mako guda kenan da ake fuskantar ƙaranci da tsadar man fetur a Najeriya, wanda hakan ya tilastawa masu ababen hawa ƙara kudin sufuri.

 

 

 

Da yawa daga cikin ƴan kasar kuwa wasu sun ajiye ababen hawansu sakamakon karancin ma da ake fuskanta.

 

 

 

Sai dai a jiya gwamnatin tarayya ta ce zuwa yau Laraba za ta kawo karshen wahalar ma fetur da ake fuskanta.

 

 

 

Sai dai har kawo yau ɗin an ci gaba da fuskantar matsi da tsadar man duk da cewar gwamnatin ta sha alwashin kawo karshen matsalar

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: