Gamayyar kungiyoyi  daban daban ne suka ziyarci fadar shugaban kasa a ranar litinin, sakamakon karuwar rasa rayuka da ke aukuwa a jihar zamfara.

Ziyarar wadda aka gudanar bias jagorancin shugaban gamayyar kungiyoyin  Usman Balarabe da matar gwamnan jihar Kaduna Asia Muhammad Ahmad, awanni 48 bayan kisan gilla da aka yiwa mutane a jihar Sokoto.

Gamayyar kungiyoyin sun nuna damuwarsu matuka ganin yadda kasha kashen rayuka ke kamari a jihar zamfara da ma wasu makotan jihar.

Sai dai shugaba muhammadu buhari ya bayyana aniyar daukar tsauraran matakai don hukunta wadan ke da hannu a ciki, tare da kawo karshen matsalar tsaro a jihar da ma kasa baki daya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: