Shugaban hukumar tace fina finai da ɗab’i a jihar Kano Mallam Isama il Na’abba Afakallahu ya bayyana cewar bhukumar ba ta hana Adam Zango zuwa kano kallom fim ba.

Afakallahu ya ce a sanarwar da jarumin ya yi ya nuna cewar zai yi wani kwarya kwaryar wasa ne kuma hakan ce ta sa yin gargaɗi a kansa saboda rashin cika ƙa idar da hukumar ke da shi.

Cikin zantawarsa da Mujallar Matashiya Afakallahu ya ce babu wani yunƙuri na hanashi zuwa kallom fim sai don bayyana cewar yana son ganawa da masoyansa tare da raba musu kyautuka wanda hakan yayi dai dai da keta dokar hukumar muddin bai nemi sahalewar hakan ba.

A gefe guda kuwa Afakallahu ya musanta zargin da jarumin yayi na cewar hukumar na haɗa kai da wasu mutane a masana antar don dadidhe tauraruwarsa a masana antar wanda ya ce ” An sanka ba sanin shanu ba, kuma kowa ya san yadda kake kuma jama a ne za su yi alƙalanci a kanka” inji Afakallah.

Jarumin dai ya bayyana cewar ya fita daga masana antar gaba ɗaya har ma yayi zargin cewar ko da ya je hukumar don yin rijista to kuwa hakan ba zai yi maganin matsalar da yake fuskanta ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: