Hukumar kula da ƙananan yara ta majalisar dinkin duniya UNICEF ya ce a Najeriya an yi garkuwa da ɗalibai dama da dubu ɗaya.

A wani rahoto da hukumar ta tattara a kan yadda ƴan ta’adda ke kai hare-hare makarantu tare da sace ɗalibai.

Hukumar ta ce akwia yuwuwar fargabar sace ɗaliban ya yi sanadiyyar raba yara miliyan ɗaya daga makarantu.

Daga cikin makarantun da hukumar ta tattara alkaluman tare da fitar da hasashen akwia makarantun firamare da sakandire da kuma ɗaliban jami’a.

Hukumar ta ce fargabar rashin tsaro ce za ta yi silar raba mutanen daga makarantn.

Akwai ɗalibai da dama da ke hannun yan bindiga waɗanda aka sace daga makarantu daban-daban na jihohin ƙasar musamman ma arewaci.

Satar ɗalibai tare da neman kuɗin fansa wani saloo ne da yan bindigan su ka ɗauka daga baya, bayan ɗauki ɗaiɗai da su ke yi wa mutane a cikin gari ko kan tituna.

Leave a Reply

%d bloggers like this: