Connect with us

Labarai

Gobara Ta Hallaka Uwa Da Ɗanta A Kano

Published

on

Hukumar kashe gobara ta ce wasu mutane biyu sun rasa ran su a sanadiyyar wata gobara data tashi a wani gida da ke kan hanyar zuwa Gwarzo.

Zainab Yusha’u da ɗan mai shekaru 25 a duniya da ɗan ta Sulaiman Usaini mai shekara ɗaya sun rasa ran su yayin da gobarar ta cimmusu.

Lamarin ya faru a safiyar yau kuma hukumar ta samu nasarar kashe gobarar.

Hukumar ta ja hankalin mutane da su ƙara kula da al’amuran wuta musamman a wannan lokaci na sanyi domin hana afkuwar tashin gobara.

A wani labarin kuma hukumar kashe gobara a jihar Kano ta gano gawar wani mutum mai kimanin shekaru 50 a duniya.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar Saminu Yusif ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.

Ya ce sun samu kiran waya daga wani Jamilu Harisu wanda ya sanar da su sun ga wani mutum a bakin wani ruwa a unguwar Sallari.

Jami’an sun isa wajen a yau bayan karɓar kiran da su ka yi sannan su ka iske mutumin yashe a gefen ruwan.

Saminu Yusif ya ce bayan riskar mutumin daga bisani aka tabbatar ya mutu.

Tuni hukumar kashe gobara ta Kano ta miƙa gawar mamacin ga baturen ƴan sanda na Filin Hokey domin faɗaɗa bincike.

Har lokacin da mu ke kammala wannan labari ba mu ji bayani daga jami’an tsaron a kan musabbabin mutuwar mutumin ba.

 

 

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Zagon Kasan Da Kwankwaso Ya Yi Wa Jam’iyyar NNPP Ya Sa Ba Muyi Nasara A Kotuba- Alhaji Abbas

Published

on

Babban jigo a jam’iyyar NNPP, Alhaji Abbas Onilewura ya zargi dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso kan rasa nasarar jam’iyyar a jihar Kano.

 

A jiya Laraba 20 ga watan Satumba kotun ta yanke hukunci inda ta tsige Gwamna Abba Kabir na jam’iyyar a matsayin gwamna.

 

Kotun kuma ta tabbatar da Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

 

Yayin da ya ke martani kan hukuncin, Abbas ya ce Kwankwaso ya siyar da jam’iyyar lokacin da ya ke tattaunawa da APC kan mukamin minista a Abuja.

 

Onilewura ya bayyana haka ne a yau Alhamis 21 ga watan Satumba a cikin wata sanarwa da ya fitar.

 

Ya ce zagon kasa da Kwankwaso ya yi wa jam’iyyar ce ya jawo rashin nasararta a hukuncin kotun da aka yanke a jiya.

 

Ya kara da cewa Wannan rashin nasara babbar asara ce a jam’iyyar mu kuma hakan ya faru ne saboda son rai na Kwankwaso wanda ya siyar da jam’iyyar.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Delta Ta Amince Da Rage Kaso 25 Na Kudin Jami’a A Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Delta ta amince da rage kashi 25 na kudin makarantar daliban jami’a a jihar.

Wannan dai wani bangare ne na tallafin da gwamnatin za ta bai wa daliban kuma ya shafi jami’a hudu mallakin jihar.

Hakan na kunshe a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Festus Ahon ya sanyawa hannu ranar Laraba.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bayar da umarnin bai wa ma’aikatan jihar tallafin naira dubu goma kowanne tsawon watanni uku.

Sannan an amince da kashe naira biliyan 5.522 ga ma’aikata 50,196 a matsayinalawus da aka yi musu karin matsayi.

Sannan gwamnatin za ta kashe naira biliyan goma wajen raba buhun shinkafa 17,000 da sama da buhu masara 60,000 ga marasa karfi.

Continue Reading

Labarai

Cibiyar Kare Hakkin Yan Jaridu Ta Yi Allah-Wadai Da Cin Zarafin Yan Jarida A Kano

Published

on

Cibiyar kare hakkin yan jarida ta duniya ta yi Alla wadai da cin zarafin yan jarida da wasu yan sanda su ka yi a Kano yau Laraba.

Salim Umar na jaridar Daily Trust da Zahradden Lawal na jaridar BBC an ci zarafinsu tare da lalata layan aikinsu yayin da us ke bakin aiki.

Babban jami’in kare hakkin yan jarida na duniya Melody Akunjiyan ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai a yau.

Cibiyar ta ce abin takaici ne ganin yadda yan sandan su ka nuna rashin kwarewa ta hanyar cin zarafin yan jaridan yayin da su ke bakin aiki.

Cibiyar ta bukaci hukumar yan sanda ta kasa da su kula tare da kiyayewa a gaba wajen cin zarafin yan jarida musamman idan aiki ya hadasu da jami’an yan sanda.

Haka kuma cibiyar ta bukaci da aka ci gaba da bai wa yan sanda horo yadda za su dinga mu’amala da yan jarida tare da mutunta darajar dan adam.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: