Connect with us

Labarai

Lassa Ta Hallaka Mutane 40 A Watan Janairu A Najeriya

Published

on

Hukumar hana yaduwar cutuka masu yaduwa a Najeriya NCDC ta ce mutane 40 ne su ka rasa rayukansu a sakamakon cutar Lassa a watan Janairun da ya gabata.

A rahoton halin da ake ciki a dangane da ctar wanda hukumar ta saba fitarwa, hukumar ta ce an samu ƙaruwar mutuwar mutane da kashi 22.2 cikin ɗari.

Rahoton ya tabbatar da cewar akwai wasu mutane 211 da aka tabbatar su na ɗauke da cutar Lassa yayin da ake zargin mutane 981 sun kamu da cutar.

Kashi 80 cikin ɗari na mutanen da aka tabbatar su na ɗauke da cutar sun fito ne daga jihohin Edo, Bauchi, da jihar Ondo.

Hukumar NCDC ta ce an samu masu ɗauke da cutar a jihohi 14 na Najeriya.

Sai dai hukumar ta ce a rahoton da ta tatara na watan Janairun shekarar da mu ke ciki babu wani ma’aikacin lafiya da ya kamu da cutar.

Sa’annan dukkanin hukumomin da aka tanada don yaki da cutar na aiki tuƙuru don ganin an kawo ƙarshenta baki ɗaya.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mutane A Fadar Sarki A Zamfara

Published

on

Wasu da ake zargi yan bindiga ne sun kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu da dama a jihar Zamfara.

 

Harin da su ka kai a jiya da daddare, sun lalata karfen sadarwa na kayin waya wanda hakan ya hana damar sadarwar a garin.

 

Yaan bindigan sun kai hari garin Dauran a ƙaramar hukumar Zurmi ta jihar

 

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Yazid Abubakar ya tabbatar da faruwar hakan yau Alhamis.

 

Ya ce mutane uku aka kashe a garin yayin da aka yi garkuwa da wani mutum guda.

 

Sannan sun kone wata tashar sadarwar layin kira na MTN a garin.

 

Ƴan bindigan sun shiga garin dauke da muggan makamai.

 

Mazauna garin sun shaida cewar an kashe mutane uku sannan an yi garkuwa da wasu mutane da ba a kai ga ganosu yawansu ba a masarautar Zurmi.

 

A garin na Dauran kuwa, an yi garkuwa da mutane biyar

 

 

Continue Reading

Labarai

An Kama Masu Garkuwa Da Mutane Biyu Tare Da Dakile Wasu Hare-Hare A Sokoto, Kaduna Da Filato

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar kama wasu masu garkuwa biyu, yayin da au ka dakile wasu hare-hare a jihohin Sokoto, Kaduna da Filato.

 

Hakan na ƙunshe a wata sanarwa da su ka wallafa a shafinsu na X wato Twitter.

 

Su ka ce sun samu nasara ne a jiya Laraba.

 

Sanarwar ta ce sun tarwatsa ƴan bindigan a kauyen Sarma da ke Tangaza a jihar Sokoto.

 

Bayan wuta da su ka buɗe musu sun kuma babur, harsashi, da bindiga kirar AK47 guda ɗaya.

 

A wani cigaban kuma jami’an sun daƙile wani hari a hanyar ƙauyen Kasu da ke Kafanchan a karamar hukumar Jema’a a Kaduna.

 

A wannna waje ma sun kwato babur guda, harsashi da sauran makamai sannan su ka kama mutane biyu da su ke zargi masu garkuwa ne.

 

A wani farmakin da su ka kai a jihar Filato, a ƙaramar hukumar Barikin Ladi sun kashe ɗan fashi guda a shingen bincike da ke Kaskara.

 

 

Continue Reading

Labarai

An Sami Raguwar Yawan Haddura A Tituna Da kashi 42

Published

on

Hukumaar kiyaye afkuwar hadduta ta kasa aa Najeriya FRSC ta ce an samu raguwar haddura da kashi 42 la’akari da yadda ake samun hadduran a baya

 

Shigaban hukumar na ƙasa Dauda Biu ne ya bayyana haka a Abuja.

 

Ya ce mayar da hankali wajen tabbatar da bin kaidar tuki ya taimaka matuka wajen raguwar haddura da ake samu

 

A cewarsa, ko da a bikin salla karama da aka gaabatar a baya bayan nan,an samu raguwar haddura wanda hakan ya rage yawan mutanen da ke mutuwa.

 

Dangane da mutanen da ke mutuwa a lokutan bikin salla, an samu raguwarsu da kashi 52.5.

 

Yayin da aka samu raguwar mutanen da aka tseratar ba tare da rauni ba da kashi 43.8

 

Su kuwa mutanen da su ke samun rauni an samu ragi daa kashi 32.6, yayin da aka samu raguwar hadduran da kashi 42.5 la’akari da shekarar da ta gabata.

 

Sannan an samun raguwar masu karya dokokin tuki da kashi 14.5.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: