Connect with us

Labarai

Taɓarɓarewar Shugabanci A Najeriya Ita Ce Babbar Matsalar Ƙasar – Jega

Published

on

Tsohon shugaban hukumar zaɓe a Najeriya Fafesa Attahiru Jega y ace tsarin shugabancin da ke tafiya a Najeriya hanya ce da ƙasar ta kama wajen rugujewarta.

Farfesa Jega ya bayyana haka ne ranar Laraba a Abuja yayin wani taron da ƙungiyar ƙwadago a Najeriya ta shirya.

Jega ya ce tsarin mulkin da ake gudanarwa a Najeriya a yanzu tamkar ana tafiya ne a makance domin babu hanyar da aka nufa ta gyara illa taɓarɓarewar tsarin shugabancin.

Taron da aka shirya domin duba makomar tsarin shugabancin da ake gudanarwa a halin yanzu da kuma zaɓen da aka tinkara na shekarar 2023, Jega ya ce tattalin arziƙi a halin yanzu ya yi rauni a ƙasar kuma duk hakan na da alaƙa da rashin kyakkyawan shugabanci na gari.

Sannan ya ce tsarin shugabancin ba zai ci gaba ba har sai an samar da haɗin kai a tsakanin ma’aikata tare da fitar da manufa mai kyau wanda ya ce hakan zai taimaka wajen samar da nasara domin magance matsalolin da ake fusknata a ƙasar a halin yanzu.

Jega ya bayyana yadda ake samun koma baya a wajen walwalar jama’a, tsaro da tattalin arziƙin ƙasa wanda hakan ya zamto babban ƙalubale da ake fusknata  a halin yanzu.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Rundunar Sojin Sama Ta Yi Nasarar Hallaka Yan Ta’adda Da Dama A Borno

Published

on

Rundunar sojin saman Najeriya ta samu nasarar hallaka yan ta’adda da dama a wani aikin haɗin gwiwa da su ja yi ƙarƙashin Operation Haɗin Kai.

 

 

 

A wata sanarwa da ta fitar yau Laraba, rundunar ra ce ta lalata maɓoyarsu a ƙananan hukumomin Damasak da Mobbar a jihar Borno.

 

 

 

Mai magana da yawun sojin saman Najeriya Edward Gabkwet ya ce ƴan ta’addan na shirin kaiwa jami’an hari a Lada iyaka da e tsakanin Najeriya da Nijar.

 

 

 

Ya ce maharan na kan hanyar tasu kan babura ne kuma aka gano maɓoyarsu a wasu wuri biyu na kauyen Zarri nisan kilomita 28 zuwa ƙaramar hukumar Damasak da Mala a ƙaramar hukumar Mobbar.

 

 

 

Bayan bibiyarsu da aka yi su ka ahirya tawaga ƙarƙashin Operation Haɗin Kai a jiya Talata.

 

 

 

Bayan hallakasu ne kuma su ka lalata sansanin da su ke shirin kafawa

 

 

 

Hukumar ta gano cewar maharan sun ketaro ne daga ƙasar Nijar da nufin kafa sansani a yankunan da aka cimmusu

 

 

Continue Reading

Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Uku Sun Sace Mutane Takwas A Kaduna

Published

on

Wasu da ake zargi masu garkuwa ne sun kashe mutane uku tare da yin awon gaba da wasu Takwas a jihar Kaduna.

 

 

 

Lamarin ya faru a ƙauyen Hayan Habuja da ke gujdumar Kakangi a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar.

 

 

 

Wannan na zuwa ne kwana biyar bayan da ƴan bindiga su ka kashe mutane 23 a Anguwan Danko kusa sa garin Dogon Dawa a ƙaramar hukumar Birnin Gwari.

 

 

 

An kashe mutanen a jiya Talata da misalin ƙarfe 03:00pm na rana kamar yadda shugaban ƙungiyar masarautun Birnin Gwari Abdurrashid Abarshi ya bayyanawa gidan talabiji na Channels.

 

 

 

Ya ce an harbe mutane biyu kai tsaye a wajen yayin da su ka tafi da mutane huɗu.

 

 

 

Ya ƙara da cewa yayin da ƴan bindgan ke kan hanyarsu ne a ƙauyen Hayin Habuja su ka sake awon gaba da wasu mutane huɗu bayan sun kashe mutum guda

 

 

 

Ya ce waɗanda aka tafi da su a kan hanyar sun dawo ne daga yin itace a daji.

 

 

 

Ko da aka tuntuɓi jami’an yan sanda a jihar dangane da faruwar lamarin, ba su ce komai a kai ba.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Sauke Hakimai 15 A Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Sokoto ta sauke wasu hakimai 15 a jihar bayan samunsu da hannu a aikata ta’addanci, siyar da kadarorin gwamnati da saɓawa dokokin aiki.

 

 

 

Gwamnan jihar Ahmad Aliyu ne ya bayar da umarnin saukesu bayan da wani kwamiti ya yi aiki a kansu kan zargin da ake yi musu.

 

 

 

Sakataren yaɗa labaran gwamnan Malam Abubakar Bawa ya bayyanawa manema labarai cewa, an samu shugabannin ne da saɓawa dokoki, hannu da aikata garkuwa da mutane, sa kuma mallakawa daidaikun mutane wajen gwamnati.

 

 

 

Sannan gwamnatin ta sauyawa wasu hakimai wurin aiki wanda ya haɗa da Binji, Sabon Birni da Bumkari.

 

 

 

Haka kuma an umarci wasu hakimai biyu su koma matsayinsu.

 

 

 

A baya, gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti da zai yi bincike dangane da zarge-zargen da ake yi wa hakiman, kuma bayan kammala bincike aka ɗauki mataki a kansu.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: