Connect with us

Labarai

CAN Sun Jaddada Ƙin Goyon Bayan Tikitin Takarar Musulmi Da Musulmi A Najeriya

Published

on

Kungiyar kiristoci ta Najeriya CAN a jihohin arewa 19 da Abuja, ta sake jaddada rashin amincewarta da tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC musulmi da musulmi.

Babban sakataren kungiyar Cristian Sunday Oibe, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a jihar Kaduna, watanni kadan gabanin zaben shugaban kasa.

Bayan nasarar da ya samu a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC, Sanata Bola Tinubu – musulmi – ya bayyana Sanata Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa a zabe mai zuwa.

Shettima, wanda ya taba zama gwamnan jihar Borno karo biyu, musulmi ne daga yankin arewa maso gabas, kuma dan majalisa mai wakiltar Borno ta tsakiya a majalisar dokokin tarayya da ke Abuja.

Shugaban kungiyar ta CAN ya kuma bayyana damuwarsa kan matsalar rashin tsaro da ke addabar sassan kasar nan, inda ya ce babu wanda zai tsira idan ‘yan ta’adda za su yi barazanar sace shugaban kasa da Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna.

Don haka ya bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya tashi tsaye wajen gudanar da wannan abu ta hanyar sauke nauyin da kundin tsarin mulki ya dora masa na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa da kuma kare martabar Najeriya.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Sojojin Najeriya Sun Gano Rijiyoyin Danyen Man Fetur Biyar Da Barayi Su Ka Yi A Rivers

Published

on

Rundunar sojin Najeriya sun gano rijiyoyin mai biyar da barayin danyen mai suka haka a jihar Ribas.

Sojojin sun sanar da kama masu satar danyen man ne da litar mai 45,000 a jiya Laraba, 15 ga watan Mayu.

Da yake jawabi a madadin kwamandan rundunar, Laftanal Kanal Ishaya Manga ya ce barayin danyen man suna amfani da tukwane wurin tace shi.

Laftanal Kanal Ishaya Manga ya kara da cewa nasarar da suka samu ta samo asali ne daga farautar barayin da suka fara tun watan Fabrairu.

Ya tabbatar wa yan jarida cewa akwai wasu ramukan da bata garin suke cigaba da boye danyen mai a ciki amma sannu a hankali rundunar za ta cimma musu.

Laftanal Kanal Ishaya Manga ya yi godiya ga mutanen yankin kan cigaba da goyon baya da suke basu wurin yaki da barayin.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Hukumomi A Legas Za Su Tsabtace Gine-Gine Da Akai Ba A kan Ka’ida Ba

Published

on

Hukumomi a jihar Lagos sun dauki gagarumin aikin tsaftace gine-ginen da aka yi ba bisa ka’ida ba a yankin Lekki.

Kwamitin kar-ta-kwana da Gwamnatin jihar ta kafa domin gudanar da aikin karkashin jagorancin CSP Shola Jejeloye zai rushe dakunan da aka gina a yankin.

CSP Shola Jejeloye ya bayyana cewa idan an rushe daruruwan gine-ginen, ana sa ran zai taimaka wajen kakkabe ayyukan bata-gari a yankin.

Shugaban kwamitin kar-ta-kwana, CSP Shola Jejeloye ya bayyana cewa sun kama wasu masu babura da ke bin titunan Victoria Island, da Bourdillon.

Haka zalika baburan suna bin hanyoyin Falomo, da Ikeja, da Abeokuta Expressway, da Ojodu Berger, da Fagba, duk da hana su da gwamnati ta yi.

Ya ce an kama baburan haya guda 220, kuma za su ci gaba da tilasta cewa matuka baburan har sai an bi dokar gwamnati.

CSP Shola Jejeloye ya gargadi matuka baburan da su guji karya dokar gwamnati domin tsaftace hanyoyin da ke jihar Lagos.

Continue Reading

Labarai

Atiku Ya Yi Martani Kan Kudin Yan Fansho Da Tinubu Zai Yi Amfani Da Su

Published

on

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi martani ga gwamnatin Bola Tinubu kan karkatar da kuɗaɗen ƴan fansho.

Gwamnatin ta bayyana kudurin amfani da kudaden yan fansho ne domin ayyuka na musamman wajen raya kasa.

Sai dai lamarin ya samu suka a wurin masana da yan siyasar Najeriya.

Hukuma mai kula da kudaden ƴan fansho ta kasa ta sanar da cewa asusun kuɗaɗen fansho ya kai Naira tiriliyan 19.96.

Ministan kudi na kasa, Wale Edun ne ya bayyana cewa gwamnatin za tayi amfani da kudaden wajen yin ayyukan raya kasa.

A cewar ministan za a yi amfani da kuɗaɗen ne domin samar da wadatattun gidaje a Najeriya.

Sai dai masana harkokin kudi sun nuna cewa tsarin dokar kasa bai ba gwamnatin damar amfani da kuɗin ma’aikata ba.

Wani masanin harkokin kudi, Musa Ibrahim ya bayyana cewa cikin abubuwan da doka ta ba gwamnati damar yi da kuɗaɗen yan fansho babu ayyukan da ya ke kokarin yi yanzu.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: