Lafiya
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya


Wannan shafi da ke kawo muku rahoto na musamman a ciki, a wannan watan ma muna ɗauke da wani rahoto wanda zai mai da hankali kan yadda ake gudanar da auratayya ba tare da gwajin jini ba, duk da irin kiraye kirayen da jami’an lafiya ke ta ya kan a dinga gwajin jini kafin aure.

A baya dai iyaye da kakanni basu san wani abu ba wai shi gwajin jini kafin aure ba, sun kasance suna yin aure ne bisa tafarkin biyayyar iyaye ko kuma soyayya a tsakanin junansu.
Sai gashi a yanzu ana ta gudanar da maƙaloli da kuma gangami, har da kiraye kiraye a masallatai kan a dinga gwajin jini kafin aure, duk da ba kasafai ake amsa kiraye kirayen ba kasancewar Al’umma na tsoron zuwa a gwada jininsu don gudun haifar musu da matsala akan neman auren da suke.

Wannan gwajin jini da ake ta kiraye kiraye aje ayi ba lallai sai gwajin HIV Ba ana zuwa gwaji don sanin matsayin jinin halittarka, saboda sanin wa ya dace ka aura wacce zaku dinga haifan ƴaƴa lafiyayyu ba tare da wasu ƙwayoyin cututtukan da zai dinga wahalar dasu .

Sai dai wani abin da ke wahalar da masoya a wannan lokaci shine sai bayan sun shaƙu da juna wata ƙila sai ana dab da yin auren su, sai ace suje su gwada jini don gudun faɗawa matsala, wanda daga ƙarshe idan aka samu sakamakon da bai yi musu daɗi ba sai ya zama sun shiga wani yanayi na rashin son rabuwa da juna.

Kamar yadda ta faru da wasu masoya, Suleman da Maryam suna son junansu anyi maganar aure, sai iyaye suka bada shawara akan suje su gwada jininsu, da aka bincika sai sakamako ya nuna cewa Suleman da Maryam suna ajin AS ne wato akwai yaƙinin zasu iya haifar ƴaƴa masu dauke da cutar Sikila (sickler).
Wanda kamata yayi ace AS ya auri AA, ko kuma mai SS Ya auri AA, shine za’a dinga haifar lafiyayyun ƴaƴa.

A yanzu haka dai sun kasa rabuwa da juna kasancewar sun shaƙu sosai suna ganin idan suka rabu ba lallai ita ta samu wanda take so ba, haka shima abin da yake tunani kenan, wannan shine abin dake haifar da matsala akan gwajin jini kafin aure.
Haka zalika Mujallar Matashiya taji ta bakin wasu matasa inda wani matashi Abubakar mai laƙabin Ɗan Beauty ya bayyana cewa shi bazai iya haƙura da yarinyar da yake so ba, idan har aka gano cewa jininshi da nata ka iya haifar da matsala idan suka yi aure ta hanyar Haifar ƴaƴa marasa lafiya.
A cewar ɗan Beauty shi so wani abu ne wanda idan aka fara shi to babu rabuwa sai dai mutuwa ta raba, amma cuta ko wani abu bazai sa ya ja baya ba kan soyayyarsa.
Ita kuwa Aisha Humaira ta bayyana cewa ita zata iya rabuwa da saurayinta muddin aka gwada jininta aka tabbatar zasu iya jefa ƴaƴansu cikin wani yanayi, to gwanda su hakura Allah ya haɗa kowa da rabonsa.
Ta ƙara da cewa ana aure ne don raya sunna tare da haifar ƴaƴan da zasu taimakeka, to idan ka haifi ƴaƴa ba lafiya kenan zaku kasance ne kullum cikin ɗawainiyar zuwa asibiti, wanda ba haka aka so ba, gwanda tun farko a magance matsalar tun kafin a shiga.
Shima wani ƙwararran likita mai zaman kansa Dr Ibrahim mohammad ya bayyana cewa gwajin jini abu ne mai kyau musamman ga masu shirin aure don gudun faɗawa matsala ta hanyar haifar ƴaƴa marasa cikakken lafiya.
Haka zalika gwajin HIV shima abu ne da ya dace masu shirin aure su dinga yi, amma dai sanin matakin rukunin da jininka yake abu ne da ya dace don gano macen da zaka aura, haka ita ma ta gano irin mijin da zata aura bayan an bincika halayensa na nagari da mu’amalarsa a cewar Dr Ibrahim.
Ga yadda rukunin jini yake da kuma yadda masu son yin aure ya kamata su kasance.
AA+SS = Yayi dai dai
AA+AA= Yayi dai dai
AA+AS= Ba damuwa
AS+AS= Bai yi ba
AS+SS = Da matsala
SS+SS= bai yi ba kwata kwata.
Wannan sune na’uikan ajujuwan jinin mutane da yadda ya kamata su auri juna.
Lafiya
Cikin Shekaru Biyu Korona Ta Hallaka Mutane Dubu Uku A Najeriya


Hukumar lura da dakile cutyka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce mutane dubu uku ne su ka rasa rayukansu a sanadiyyar cutar Korona.

A wata sanarwa da hukumar ta fita, ta ce sama da mutane dubu ɗari biyu aka samu sun kamu da cutar, sai dai fiye da kashi 80 cikin 100 sun warke kuma an sallamesu.
Hukumar ta ce ta samu wasu darrusa na dakile cutuka masu yaɗuwa tun bayan ɓullar annobar Korona da cutar Lassa.

Sai dai a wannan lokaci hukumar ta mayar da hankali ne a kan cutukan Lassa da cutar amai da gudawa wato Kwalara wadda ke ci gaba da yaɗuwa a wasu jihohin Najeriya.

A ranar 27 ga watan Fabrarun da ya gabata ne dai aka cika shekaru biyu cif da ɓullar cutar Korona a Najeriya wadda ta yi sanadiyyar rasa rayuwar mutane dubu uku a faɗin ƙasar.


Lafiya
Ƙasa Da Mutane Miliyan Goma Aka Yi Wa Riga-Kafin Korona A Najeriya


Hukumar lafiya matakin farko a Najeriya ta ce ƙasa da mutane miliyan goma kadai aka yi wa riga-kafin cutar Korona a fadin ƙasar baki ɗaya.

Shugaban hukumar Dr. Faisal Shu’aib ne ya bayyana haka ya ce a ranar 25 ga watan Fabrairun da mu ke ciki alƙaluma sun nuna cewar mutane miliyan 8,145,416 ne su ka karbi riga-kafin cutar.
Wannan na nuni da cewar ba a ɗauki hanyar cimma kson da hukumar lafiya ta duniya ke son kai wa na yi wa adadi sama da 80 cikin ɗari riga-kafin ba.

Dr. Faisal Shu’aib ya ƙara da cewa a ranar 25 ga watan Fabrarun, akwai mutane miliyan 17,646,781 da aka yi wa riga-kafin farko ba a yi musu maimai ba.

Haka zalika a ƙasar, an tabbatar da cewar mutane 254,428 su kamu da cutar yayin da aka gwada mutane 4,317,621 da ake zargi.

Daga cikin mutane sama da miliyan 200 da aka samu su na ɗauke da cutar tuni aka sallami fiye da kashi 70 cikin 100 daga cikinsu bayan an ba su kulawa sannan aka tabbatar sun warke daga cutar.
Faisal Shu’aib ya ce akwai buƙatar sake sabon salo don ganin an cimma kaso na adadin mutanen da ake so a yi wa riga-kafin cutar bisa umarnin hukumar lafiya ta duniya domin kawo ƙarshen cutar a fadin duniya.

Labarai
Najeriya Na zata samar da Maganin Gargajiya na Korona


A yayin da kasashen Turai ke cigaba da yin gwaje-gwaje ingancin maganin Korona da suka hada, Najeriya ma ba a barta a baya ba wajen hadawa da yin nata gwajin magungunan.

Sai dai Hukumar kula da Ingancin Abinci Da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) ta bayyana cewa tana yin gwajin magungunan warkar da Korona har guda 40 da masu hada magungunan gargajiya suka mika wa hukumar.
Shugabar hukumar Mojisola Adeyeye ta sanar da haka tana mai cewa ana yin gwajin ingancin magungunan ne saboda tabbatar da ingancin maganin da Alumna zasu yi amfani dashi.

” Haka kuma NAFDAC ta gindaya musu wasu sharudda da dokoki da za su bi wajen hada maganin.

Za dai a fara a yin gwajin ingancin magungunan akan dabbobi a karon farko tukunna.

Mojisola ta gargadi masu maganin kada su kuskura su jaraba wani magani ba tare da hukumar ta bada daman haka ba.

-
Labarai1 week ago
Da Ɗumi-Ɗumi A Na zargin Bam Ya Tashi a Unguwar Sabon Gari A Kano Yanzu
-
Labaran jiha1 week ago
Ƴan Bindiga Sun Hallaka Mutane Shida Sun Tafi Da Sarkin Garin Ƙarfi Dake Jihar Kano
-
Labarai2 weeks ago
ASUU Ta Janye Yajin Aikin Da Ta Ke Yi
-
Labarai2 weeks ago
INEC Ta Sanar Da Ranar Rufe Yin Rijistar Katin Zaɓe
-
Labarai4 days ago
Za’a Daina Anfani Da Kuɗin Takarda A Najeriya – CBN
-
Labarai6 days ago
Sabuwar Ƙungiyar Ta’addanci Ta Ɓulla A Kaduna
-
Labarai2 weeks ago
An Rufe Makaranta Bayan Ƙone Ɗaliba Da Ranta Bisa Ɓatanci Ga Annabi A Sokoto
-
Labarai2 weeks ago
Jihohi 32 A Najeriya Na Iya Fuskantar Mummunar Ambaliyar Ruwan Sama A Bana