Lafiya
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya


Wannan shafi da ke kawo muku rahoto na musamman a ciki, a wannan watan ma muna ɗauke da wani rahoto wanda zai mai da hankali kan yadda ake gudanar da auratayya ba tare da gwajin jini ba, duk da irin kiraye kirayen da jami’an lafiya ke ta ya kan a dinga gwajin jini kafin aure.

A baya dai iyaye da kakanni basu san wani abu ba wai shi gwajin jini kafin aure ba, sun kasance suna yin aure ne bisa tafarkin biyayyar iyaye ko kuma soyayya a tsakanin junansu.
Sai gashi a yanzu ana ta gudanar da maƙaloli da kuma gangami, har da kiraye kiraye a masallatai kan a dinga gwajin jini kafin aure, duk da ba kasafai ake amsa kiraye kirayen ba kasancewar Al’umma na tsoron zuwa a gwada jininsu don gudun haifar musu da matsala akan neman auren da suke.

Wannan gwajin jini da ake ta kiraye kiraye aje ayi ba lallai sai gwajin HIV Ba ana zuwa gwaji don sanin matsayin jinin halittarka, saboda sanin wa ya dace ka aura wacce zaku dinga haifan ƴaƴa lafiyayyu ba tare da wasu ƙwayoyin cututtukan da zai dinga wahalar dasu .

Sai dai wani abin da ke wahalar da masoya a wannan lokaci shine sai bayan sun shaƙu da juna wata ƙila sai ana dab da yin auren su, sai ace suje su gwada jini don gudun faɗawa matsala, wanda daga ƙarshe idan aka samu sakamakon da bai yi musu daɗi ba sai ya zama sun shiga wani yanayi na rashin son rabuwa da juna.

Kamar yadda ta faru da wasu masoya, Suleman da Maryam suna son junansu anyi maganar aure, sai iyaye suka bada shawara akan suje su gwada jininsu, da aka bincika sai sakamako ya nuna cewa Suleman da Maryam suna ajin AS ne wato akwai yaƙinin zasu iya haifar ƴaƴa masu dauke da cutar Sikila (sickler).
Wanda kamata yayi ace AS ya auri AA, ko kuma mai SS Ya auri AA, shine za’a dinga haifar lafiyayyun ƴaƴa.
A yanzu haka dai sun kasa rabuwa da juna kasancewar sun shaƙu sosai suna ganin idan suka rabu ba lallai ita ta samu wanda take so ba, haka shima abin da yake tunani kenan, wannan shine abin dake haifar da matsala akan gwajin jini kafin aure.
Haka zalika Mujallar Matashiya taji ta bakin wasu matasa inda wani matashi Abubakar mai laƙabin Ɗan Beauty ya bayyana cewa shi bazai iya haƙura da yarinyar da yake so ba, idan har aka gano cewa jininshi da nata ka iya haifar da matsala idan suka yi aure ta hanyar Haifar ƴaƴa marasa lafiya.
A cewar ɗan Beauty shi so wani abu ne wanda idan aka fara shi to babu rabuwa sai dai mutuwa ta raba, amma cuta ko wani abu bazai sa ya ja baya ba kan soyayyarsa.
Ita kuwa Aisha Humaira ta bayyana cewa ita zata iya rabuwa da saurayinta muddin aka gwada jininta aka tabbatar zasu iya jefa ƴaƴansu cikin wani yanayi, to gwanda su hakura Allah ya haɗa kowa da rabonsa.
Ta ƙara da cewa ana aure ne don raya sunna tare da haifar ƴaƴan da zasu taimakeka, to idan ka haifi ƴaƴa ba lafiya kenan zaku kasance ne kullum cikin ɗawainiyar zuwa asibiti, wanda ba haka aka so ba, gwanda tun farko a magance matsalar tun kafin a shiga.
Shima wani ƙwararran likita mai zaman kansa Dr Ibrahim mohammad ya bayyana cewa gwajin jini abu ne mai kyau musamman ga masu shirin aure don gudun faɗawa matsala ta hanyar haifar ƴaƴa marasa cikakken lafiya.
Haka zalika gwajin HIV shima abu ne da ya dace masu shirin aure su dinga yi, amma dai sanin matakin rukunin da jininka yake abu ne da ya dace don gano macen da zaka aura, haka ita ma ta gano irin mijin da zata aura bayan an bincika halayensa na nagari da mu’amalarsa a cewar Dr Ibrahim.
Ga yadda rukunin jini yake da kuma yadda masu son yin aure ya kamata su kasance.
AA+SS = Yayi dai dai
AA+AA= Yayi dai dai
AA+AS= Ba damuwa
AS+AS= Bai yi ba
AS+SS = Da matsala
SS+SS= bai yi ba kwata kwata.
Wannan sune na’uikan ajujuwan jinin mutane da yadda ya kamata su auri juna.
Labarai
Buhari Ya Sake Roƙo ASUU Su Janye Yajin Aiki


Yayin da kungiyar malaman jami’o’i suka shafe akalla watanni bakwai suna yajin aiki shugaba kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci su hakura su janye .

Rahoton da aka samo ya bayyana cewa, Buhari ya bayyana hakan ne a taron bikin karrama Alhaji Muhammadu Indimi, shugaban kamfanin Oriental Energy Resources Ltd a birnin Maiduguri na jihar Borno.
An gudanar da wannan babban taro ne a cikin jami’ar Maiduguri, daya daga cikin manyan makarantun Najeriya da ke garkame sakamakon yajin da ASUU keyi.

Shugaban ya samu wakilcin shugaban ma’aikatansa Alhaji Ibrahim Gambari, wanda ya zanta kan batutuwa da yawa da suka shafi ilimi a Najeriya.

Da yake tuna batun ASUU tare da yin tsokaci a kai, Gambari ya isar da sakon Buhari da cewa

Yana da kyau su ce wani abu game da wannan yajin aikin na ASUU saboda suna karrama Alhaji Indimi wanda aka shirya wa gagarumin biki a yau domin ci gaban ilimi mai inganci da ya kawo ba a kasar nan kadai ba.
A kan haka, yana so ya isar da kiran shugaban kasa Muhammadu Buhari game da ASUU da ta janye yajin aikin da take yi, ta koma aiki.
Abangare guda, Buhari ya ce tuni tattaunawa tsakanin ASUU da gwamnati akeyi, amma duk da haka kungiyar ta ci gaba da bude makarantu.
Ya kuma koka da cewa, bai dace ASUU su ci gaba da ajiye dalibai a gida ba kasancewar abubuwa sun kasa kankama.
A cewarsa, irin wannan tsawaita wa’adin yaji na dakushe ilimi tare da kawo cikas ga ci gaban mutane.
Labarai
A Shirye Muke Don Sanya Hannu Ga Makashin Hanifa – Ganduje


Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da a shirin da take domin ganin ta yi adalci ga malamin makarantar nan, Abdulmalik Tanko da aka yankewa hukuncin kisa.

Jaridar The Guardian ta nuna Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje a shirye yake domin ganin an tabbatar da adalci ga masu laifin kisan.
Babban lauyan gwamnatin Kano, Musa Lawan ya bayyana cewa wasu suna tunanin ba za a hukunta wadanda aka samu da laifin kashe Hanifa ba.

A watannin baya ake zargin wasu mutane da laifin hallaka karamar yarinya mai shekara 5. A watan Yuli ne aka tabbatar masu da laifinsu.

A ranar Alhamis, Musa Lawan ya shaidawa mutanen Kano cewa wadanda aka yankewa hukunci za su dandana kudarsu.

Kwamishinan shari’a yake cewa hukumar gidan gyaran hali za ta bayar da shaidar tabbatar da hukunci, wanda zai fito bayan wa’adin daukaka kara.
Akwai kwanaki 90 da doka ta ba wadanda ake kara da nufin su daukaka shari’a idan ba su gamsu da hukuncin da Alkalin kotun tarayya ya zantar ba.
Idan ba a daukaka kara ba, gwamna zai sa hannu, idan kuwa an koma kotu, za a saurari shari’a.
Labarai
Lassa Ta Hallaka Mutane 158 A Najeriya


Akalla mutane 158 cutar zazzabin lasa ta hallaka a jihohi 24 a fadin kasa Najeriya cikin watanni shida na shekarar 2022 da mu je ciki.

Hukumar da ke aikin dakile cutuka masu yaduwa a Najeriya NCDC ita ce ta bayyana haka a jiya Litinin.
Ta ce mutanen da cutar ta kama sun fito ne daga kananan hukumomi 99 na kasar.

Sannan cutar tafi kama yan shekaru 21 zuwa 30 har ma zuwa masu shekara 90.

Hukumar ta ce mutane 158 sun mutu sakamakon cutar Lassa wanda hakan ke nuna karuwar cutar.

Sannan yawan waɗanda aka kara samu da cutar a wannan lokaci ya fi hauhawa a Jihohin Ondo Edo da kuma Filato.
Kuma ba a samu wani ma’akacin lafiya ba daya kamu da cutar kamar yadda aka saba samu a baya ba.
Hukumar NCDC ta ce suna nan suna aiki da ma’akatar national fever lassa multi patner domin kawo karshen cutar a kasa baki daya.
-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA