Jami’an tsaro a Jihar Zamfara sun samu nasarar kama wasu mutane masu tarin yawa wadanda ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne tare da masu kai musu bayanan sirri.

 

Jaridar Premium Times ta rawaito cewa ana zargin mutanen da aka kama sun dawo ne daga kasar Saudiyya bayan halartar aikin hajjin bana.

 

Jami’an sun kama mutanen ne a garuruwan Tsafe, Zurmi, Bungudu da kuma Shinkafi a Jihar Zamfara.

 

Wadanda ake zargin da ‘yan bindigar ne jirginsu ya sauka ne a filin sauka da tashin Jiragen sama na Sultan Abubakar na III da ke Jihar Sokoto.

 

Bayan faruwar lamarin a makon da ya gabata rahoton jaridar ya bayyana cewa jami’an da ke magana da yawun jami’an tsaron Najeriya ba su tabbatar da hakan ba.

 

Amma wasu majiyoyi da dama daga kwamitin aikin hajjin Jihar Zamfara sun tabbata da faruwar lamarin.

 

Inda suka bayyana cewa maniyyatan Jihar Zamfara na tashi ne a filin jiragen sama na Jihar Sokoto.

Leave a Reply

%d bloggers like this: