Connect with us

Labarai

Bamu Yarje A Tura Jami’an Sojin Najeriya Kasar Nijar Ba – Majalisar Dokoki

Published

on

Awannni kaɗan bayan da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya aikewa majalisar dokokin ƙasar neman sahalewar aike da dakarun soji zuwa ƙasar Nijar don ƙace mulki daga hannun sojin, shugaban ya fara shan suka ta ko ina a kan batun.

Ƙungiyar ECOWAS ta ce ba ta da waniz aɓe da ya rage illa amfani da ƙardin soja wajen karɓe ikon mulkid aga hannun sojin ƙasar Nijar, batuhn da wasu ƴan Najeriya ke yin watsi da shi.

Ƙungiyar Sanatocin Arewacin Najeriya ta barranta kanta daga amincewar hakan tare da kira domin samun wata mafitar maimakon amfani da soja wajen karɓar mulkin.

Ko a ɓangaren malamai a Najeriya daban-daban na bayyana rashin dacewar hakan domin hakan na iya haifar da wata ƙiyayya da matsalar da ba a san ƙarshenta ba.

Dakta Snai Umar Rijiyar Lemo a Kano na daga cikin malaman da su ka soki batun tare da nuna rashin goyon baya a kai.

Mutane na kira ga shugaban ƙungiyar ECOWAS kuma shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da a sauya dabara, domin amfani da ƙarfin soja wajen ƙwatar mulki a Nijar ba mafita ba ce.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nemi amincewar majalisar a wata wasiƙa da ya aike musu a ranar Alhamis, wanda kuma shugaban majalisar Godswill Akpabio ya karantata.

Ƙungiyar ECOWAS na nemo dabarun ƙace mulki, bayan da masu mulki a Nijar ɓangaren soja su ka hyi watsi da tayin sulhu da wakilcin su ka je garesu a ranar Juma’a.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mafarauta 18 A Taraba

Published

on

Ƴan bindiga sun kashe mafarauta 18 a wani harin da suka kai a ƙaramar hukumar Bali da ke jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe mafarautan 15 ne a wata arangama da ƴan bindiga a wani dutse kusa da garin Maihula a ranar Talata, 28 ga watan Nuwamba.

An ruwaito cewa ƴan bindigan da yawansu ya haura 200 sun yi yunƙurin kai hari a garin Bali Shalkwatar ƙaramar hukumar Bali, da wasu ƙauyukan da ke kewaye amma mafarautan sun yi artabu da su.

Ƴan bindigan waɗanda suke ɗauke da miyagun bindigu da suka fi na mafarautan, sun halaka mafarauta 15 a yayin artabun.

Wata mazaunin yankin mai suna Musa Umar ya bayyana cewa, mafarauta 14 ne suka mutu a wurin artabun, yayin da wasu mafarauta da dama suka samu raunuka, ɗaya kuma ya mutu a hanyar zuwa Asibitin Jalingo wanda adadin ya kai 15.

Shugaban kungiyar mafarauta na jihar Taraba, Adamu Dantala ya bayyana cewa an kashe mambobinsa 15 a wata arangama da ƴan bindiga.

Ya ce ƴan bindigan sun kuma yi wa mambobinsa kwanton ɓauna a kusa da garin Dakka a ƙaramar hukumar Bali inda suka kashe mafarauta uku.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Tinubu Za Ta Inganta Tsaro Da Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Fadar Shugaban Ƙasa

Published

on

A kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2024, Bola Ahmed Tinubu ya ce babban abin da zai dage a kai shi ne tsaro da zaman lafiya a ƙasa Najeriya.

Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin samar da ayyukan yi tare da farfado da tattalin arzikin Najeriya.

A jawabin da ya gabatar, Bola Tinubu ya ce za a yiwa tsarin tsaro kwaskwarima a Najeriya domin a tsare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kundin kasafin kudin shekarar 2024 ya fi karkata zuwa ga wasu abubuwa takwas, kamar yadda mai magana da yawun shugaban ƙasa Ajuri Ngelale ya sanar a jiya Laraba.

Daga cikinsu akwai samar da hanyar da masu hannun jari za su kawo kudi domin yin kasuwanci wanda hakan zai inganta tattalin arziki.

Gwamnatin Tinubu za ta kara tsayawa tsayin-daka wajen yakar talauci da zarar an amince da kasafin kudin na 2024 a majalisun tarayya.

Kasafin kudin 2024 ya bada karfi a abin da ya shafi cigaban al’umma, musamman kananan yara wanda sai da su ake cigaba.

 

Continue Reading

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Hallaka Manoma Mutane Biyu A Taraba

Published

on

Wasu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun kashe manoma biyu a gonakinsu a yankin Yangtu a jihar Taraba.

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a kudancin jihar da ke shiyyar Arewa maso Gabas.

Tsohon ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ussa a majalisar dokokin Taraba, Habila Timothy, ya bayyana cewa manoman sun fito ne daga ƙauyen Kpambo.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa manoman sun je gonarsu da ke Kwambai, garin da ya haɗa iyaka da ƙaramar hukumar da kuma yankin Yangtu.

A nasa ɓangaren, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar yan sandan jihar Taraba, Abdullahi Usman, ya ce har yanzu rahoton bai kai ga ofishin ƴan sanda ba.

Ya kuma ƙara ba da tabbacin cewa hukumar ta ɗauki matakai kuma an yi nisa a kokarin kakkabe yan bindiga gaba ɗaya daga jihar.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: