A kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2024, Bola Ahmed Tinubu ya ce babban abin da zai dage a kai shi ne tsaro da zaman lafiya a ƙasa Najeriya.

Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin samar da ayyukan yi tare da farfado da tattalin arzikin Najeriya.

A jawabin da ya gabatar, Bola Tinubu ya ce za a yiwa tsarin tsaro kwaskwarima a Najeriya domin a tsare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kundin kasafin kudin shekarar 2024 ya fi karkata zuwa ga wasu abubuwa takwas, kamar yadda mai magana da yawun shugaban ƙasa Ajuri Ngelale ya sanar a jiya Laraba.

Daga cikinsu akwai samar da hanyar da masu hannun jari za su kawo kudi domin yin kasuwanci wanda hakan zai inganta tattalin arziki.

Gwamnatin Tinubu za ta kara tsayawa tsayin-daka wajen yakar talauci da zarar an amince da kasafin kudin na 2024 a majalisun tarayya.

Kasafin kudin 2024 ya bada karfi a abin da ya shafi cigaban al’umma, musamman kananan yara wanda sai da su ake cigaba.

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: