Gwamna Abba Kabir na jihar Kano ya nuna bacin ransa kan yadda aka saki ‘yan daba da ke kulle a jihar.

Gwamnan ya ce wannan wani mataki ne na kawo tsaiko a kokarin da gwamnati ke yi na dakile matsalar dabanci a jihar.

Abba Kabir ya bayyana haka ne yayin tarbar Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero a gidan gwamnati.

Ya bayyana yawan ‘yan dabar da aka kama domin yi musu hukunci amma abin takaici an sako su.

Har ila yau, gwamnan ya zargi jam’iyyun adawa da kokarin kubutar da ‘yan dabar domin biyan buƙatar kansu ta siyasa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: