Hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Akwa Ibom ta sanar da sakamakon zaben kananan hukumomi a jihar.

 

Hukumar ta ce jam’iyyar PDP ce ta lashe zaben kujerun da aka yi a jihar.

 

An gudanar zaɓen ne a jiya Asabar.

 

Shugaban hukumar zaben ta jihar Aniede Ikoiwak ne ya sanar da sakamakon yau a ofishin hukumar da ke jihar

 

Ya ce jam’iyyar PDP ta lashe dukkanin kujerun ƙananan hukumomi 30 a jihar.

 

Yayin da jam’iyyar APC ta lashe kujerar shugaban karamar hukuma guda.

 

Sai dai jam’iyyar APC a jihar ta yi watsi da sakamakon wanda ta yi zargin an yi magudi a zaben.

Leave a Reply

%d bloggers like this: