Tsohon dan takarar shugaban kasa a Najeriya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce ba zai tsoma baki a kan rikicin cikin gida da ya kunno kai a jam’iyyar su ta PDP ba.

Kwankwaso ya bayyana haka ne yayin da ƴan jarida su ka yi masa tambaya a gidansa da ke Kano.

Ya ce bai kamata ya saka baki a kan rikicin ba a don haka ba zai ce komai a kai ba.

A jiya ne dai shugaban jam’iyyar ya sanar da dakatar da saataren gwamnatin jihar Abdullahi Baffa Bichi da kwamishinan sufuri Muhammad Dugwal.

Sai dai daga bisani gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf ya sanar da cewar ya yi sasanci dangane da rikicin.

A wani bidiyo da ke yawo an hango Baffa Bichi na nisanta kansa daga zargin da ake masa na kirkirar wani bangare daga cikin jam’iyyar NNPP.

Ko da dai jam’iyyar ba ta fito karara ta bayyana dalilin da ya sa ta dakatar da su ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: