
Shugaban ya yi umarnin ne ga hukumar kula da jam’i’oi ta ƙasa NUC, hukumar kula da makarantun fasaha NBTE, da kuma sauran hukumomi masu ruwa da tsaki a ɓangaren.
Ya kuma umarce su da su tabbatar da an dakatar da ayyukan makarantun bogin na dindindin, don kiyaye ɓangaren ilimi da nagartarsa daga hannun gurɓatattun makarantu.

Tinubu a ƙoƙarin tabbatar da yunƙurin gwamnatinsa na inganta bangaren na ilimi, ya yi gargaɗin cewa dole ne a tabbatar da cewa ingancin ɓangaren ilimi a ƙasar nan bai gurɓata ba.

Shugaban ya yi wannan umarnin ne jiya Asabar, a wajen taron yaye ɗalibai karo na 14 na jami’ar yin karatu daga gida ta NOUN a Abuja.
Shugaban wanda ya samu wakilcin babbar darakta a ɓangaren ilimin jam’i’oi Hajiya Rakiya Gambo Iliyasu, ya buƙaci jam’i’oin da su bijiro da sabbin ƙirƙire-ƙirƙire, dan tabbatar da cewa ɗaliban da ake yayewa sun zama nagartattu.
Ya kuma ƙara da da cewa yanzu a matakin ƙasashen duniya, an mayar da tattalin arziki zuwa kan tsarin ilimi kuma bai kamata a bar Najeriya a baya ba.
Ya kuma jaddada buƙatar ganin an dakatar da yawaitar jam’i’oi na bogi, da kuma sauran makarantun gaba da sikandire a faɗin ƙasar nan.