Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya sanya hannu a kan dokar inganta rayuwar masu bukata ta musamman , wadda majalisar dokokin jihar ta zartar kwanan nan.

Gwamnan ya ce dokar za ta taimaka wajen sanyasu cikin tsare-tsaren gwamnati da suka shafi cigaban kasa.

Sannan gwamnan ya kara da cewa wanzuwar dokar ta inganta rayuwar mutanen za ta ba da damar fito da wannan bangare na alumma da nauoin bukatunsu ta yadda za a shigar da su a cikin tsarin gwamnati , tare da share musu hawaye.

Dokar dai ta hana yi musu kallon kaskanci, sannan ta yi tsari na saukaka musu rayuwa wajen shige da fice a gine-gine da maaikatun gwamnati, ga kuma tanadin da aka yi musu na wani kaso a guraben aiki.

Malam Yarima Sulaiman Ibrahim na cikin shugabannin masu bukata ta musamman a Najeriya, kuma daya daga cikin jagororinsu a jihar Kano, wanda ya ce suna murna, sakamakon sanya hannu a dokar da gwamna ya yi.

Leave a Reply

%d bloggers like this: