Babbar kotun jiha da ke zamanta a Ringim jihar  Jigawa ta yanke wa  wasu  matasa biyu Mustapha  Idris hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Da yake karanta hukuncin Alkalin kotun mai shari’a Ahmed Muhammad  Kazaure ya  ce  kotun ta samu   Mustapha Idris  da laifin  kashe wata  budurwa ta hanyar ska mata wuƙa a maƙogaronta.

Al’amarin ya faru tun a ranar 12 ga watan Janairun da muke ciki kuma kotun ta gamsu da kwararan shaidun daaka gabatar mata wanda ta samu Mutapha da kashe Nafisa Hashimu.

An yake wa Mustapha hukuncin ne ƙarƙashin sashe na 221 (a) na kundin dokokin jihar Jigawa.

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: