Wani mutum ne dan Najeriya yabar kasarsa ya tafi Amerika domin yin aiki tsawon shekara da shekaru har yayi aure a can yayi yaya amma bai dawo Najeriya ba, abinka da Amerika kome yaro yama baza ka dake shi ba saboda dokar yancin Dan Adam, yaransa sun fara girma kuma sun dame shi da rashin ji shi kuma bai iya dukansu ba saboda doka, wata rana sai ya shirya dabara, ya cewa yaran za suzo Najeriya ganin gida kuma suga kakanninsu, yara sai murna, suka shirya suka hawo zuwa Najeriya koda saukarsu a iyafot(airport) sai aka dauke wuta, can sai sauro, yara sai suka fara kuka,babansu yace baku fara kuka bama sai munje Rano.


