Mujallar Matashiya ce taga dacewar zaƙulo muku lokuta na musamman da ake karɓar addu a ciki kuwa har da lokacin da ake ruwan sama.

Kamar yadda hadisai suka tabbata cewa akwai lokuta na musamman da ake saurin karɓar addu’a ɗaya daga cikin lokutan shine yayin da ake ruwan sama.
Lokacin da ake ruwan sama a yanayin samuna ko wani lokacin da Allah ya saukar da ni imar ruwa daga sama zuwa ƙasa, lokaci ne da ake karɓar addu’ar bayi.

Sauran lokutan da ake karɓa akwai tsakiyar dare da kuma ƙarshensa wato kafin fitowar alfijir.

Haka kuma idan mutum yana tafiya ana so ya yawaita addu a shima lokacin ana karbar addu ar matafiyi da addu ar wanda aka zalunta.
Sauran sune bayan kowanne kiran sallah da kuma lokacin da liman yayi huduba ta farko a lokacin sallar juma a.
Waɗannan sune kaɗan daga cikin lokutan da ake amsar addu a idan aka yi.