Gwamnatin jihar Zamfara ta hamtawa masu riƙe da sarautar gargajiya bayar da izinin hakar ma’adinai a jihar baki ɗaya.

 

Gwamna Dauda Lawal Dare ne ya sanya hannu tare da bayar daa umarnin hanin a yayin zaman majalisar zartarwa da ya wakana yau Alhamis.

 

Cikin wata sanarwa da mia magana da yawun gwamnan Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya ce dakatarwar n adaga matakin daƙile ayyukan ta’addanci a jihar.

 

Dokar ta haramtawa masu riƙe da sarautar gargajiya bayar da izinin harkar ma’adanai ga daidaikun mutane, kamfanoni da kungiyoyi.

 

Wannan dai wani mataki ne da gwamnatin ta ɗauka a ƙoƙarin ganin an daƙile ayyukan masu garkuwa, kisan gilla da sauran ayyukan ta’addanci.

Leave a Reply

%d bloggers like this: