Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce tsauraran matakai masu wahala da ake dauka a ƙasar zai taimaka wajen cigaban kasar ne.

Tinubu na wannan jawabi ne a ƙasar China wanda ya ce ƙarin farashin da aka samu zai taimaka wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar.


Tinubu ya ce matakan da ake ɗauka na farfado da ƙasar.
Tinubu na wannan jawabi ne sakamakon ƙarin farashin man fetur da aka samu a ƙasar wanda al’umma ke kokawa.
A jihar Kwara masu ababen hawa sun yi zanga-zanga wanda hakan ya sanya matafiya yin cirko-cirko.
Sai dai gwamnatin kasar na cewar za a kawo karshen wahalarsa cikin ƙarshen mako da za mu shiga.