Sabon shugaban ƙasar Ghana John Dramani Mahama ya sha alwashin gudanar da mulki na gaskiya da adalci a ƙasar.

Mahama ya bayyana haka jiya Talata a jawabin da ya yi jim kaɗan bayan rantsar da shi.

A cewarsa zai tabbatar da inganta bangaren tattalin arzikin ƙasar

Babban mai Shari’a a kasar ne ya rantsar da shu a Black Star Square da ke Accra babban birnin ƙasar

Dubban mutane ne su ja halarta domin shaida rantsuwar.

Mahama ya mulki kasar tsakanin shekarar 2013 zuwa 2017.

Mahama ya lashe zaben da kaso 56 a ranar 9 ga watan Disamban shekarar da ta gabata.

Shugaban Najeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS Bola Ahmed Tinubu na daga cikin manyan baki na musamman da su ka halarta.

Haka kuma akwai sauran manyan shugabannin kasashen Afrika da s ka hakarta.

Leave a Reply

%d bloggers like this: