Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, ta shirya tsaf, domin mayar da wasu ababen da aka fitar daga jikin dabbobin da aka yanka a mayankar kamar su kashinsu da saurasu zuwa takin zamani.

 

Rajistaran cibiyar kula da muhallin kiwon lafiya ta kasa (EHCN) Dakta Yakubu Baba ne ya bayyana hakan a wata hirasa da Kamfanin dillancin labarai da ke babban birnin tarayya Abuja.

 

Dakta Yakubu ya ci gaba da cewa, cibiyar za ta fito da mafita inda za a rinka yin amfani da wasu ababen da aka fitar daga jikin dabbobin da aka yanka a mayankar domin sarrafa su zuwa takin zamani, inda ya kara da cewa, ana shirin yin hakan ne domin a kara samar wa da manoman kasar nan takin zamani.

 

“Cibiyar za ta fito da mafita inda za a rinka yin amfani da wasu ababen da aka fitar daga jikin dabbobin da aka yanka a mayankar domin sarrafa su zuwa takin zamani, inda ya kara da cewa, ana shirin yin hakan ne domin a kara samar wa da manoman kasar da takin zamani”.

 

A cewar Dakta Yakubu, cibiyar za ta tabbatar da an yi amfani da abababen da ake fitar wa daga jikin dabbobin da aka yanka domin ganin ba a zubar da su, inda za a mayar da su zuwa takin zamani domin amfanin manoman da ke a kasar nan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: