Connect with us

Labarai

Rashin Abba Boss Babban Giɓi Mai Wahalar Maye Gurbi

Published

on

Alhaji Muhamamd Aminu Adamu wanda aka fi sani da Abba Boss guda ne cikin jama’ar da ke talafe da rayuwar dubban mutane tare da ƙoƙarin ceto da yawa daga cikin don inganta rayuwar su.

Ya kasance ɗan kasuwa kuma manomi wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimtawa jama’a da addinin musulunci.

Mutum ne da ya ɗauki nauyin marayu wajen ciyar da su shayar da su da ma tufatar da su har ma da harkar ilimin su.

Marasa lafiya da dama ke biyawa kuɗin magani ba tare da sun san wanene ya yi ba.

Kyautata mutane ya ke yi musamman idan ya fuskanci mutum na da jajircewa wajen neman na kansa ko karatu.

Ya samar da tsarin ciyarwa don marayu da iyayen marayu da ma marayun wanda ke amfana daga lungu da saƙo na jihar Kano.

Ya na daga cikin ɗabi’un sa kyautata wa tare da mutunta Ɗan’adam wajen ganin an samar da ci gaba ta hanyar hada kai.

Mutum ne mai kishi tare da ƙoƙarin zaburar da mutane masu kishi wanda hakan ya sa ya ke kulawa da mutane da dama musamman masu ƙaramin ƙarfi wajen ganin sun tsaya da ƙafarsu.

Abba Boss ya zamto guda ɗaya tilo da ake kwatance da alherinsa a ciki da wajen yankin sa.

Kiyaye lokaci, tabbatar da adalci da gaskiya na daga cikin abubuwan da ya ke bai wa muhimmanci.

Alhaji Aminu Adamu jajirtacce ne wajen ganin an samawa talaka ƴanci wajen gudanar da tsarin rayuwa tare da ingantata.

Ya na daga cikin mutanen da ke amfani da kuɗaɗen sa don wayar da kan jama’a ta yadda za su san yancin su.

Abba Boss na daga cikin mutanen da su ka ja hankalin gwamnati yayin da aka sanya dokar kulle ta KORONA har aka sassautata wanda miliyoyin ƴan Najeriya su ka fita daga ƙangin da su ke ciki a wancen lokaci.

Hidimarsa ba ta tsaya a nan ba sai da ci gaba da yin amo don ganin ya ja hankalin gwamnati a kan yadda ake tsadar kayan masarufi tare da jan hankalin ƴan kasuwa don ganin sun rangwantawa talakawa.

Wannan kaɗan kenan daga cikin kyawawan halayen da marigayi Alhaji Muhammadu Aminu Adamu Abba Boss ya bari kuma mutane ke ƙoƙarin koyi da shi.

Ya rasu a ranar Asabar 09 10 2021 ya bar mata biyu da ƴaƴa maza da mata daga cikin iyalan sa akwai jikoki a ciki.

An yi jana’izarsa ranar Lahadi 10/10/2021 a gidansa da ke unguwar Gama (B).

Allah ya ji ƙansa da rahama idan tamu ta zo Allah ya sa mu cika da imani amin.

Abubakar Murtala Ibrahim

(Abban Matashiya)

10/10/2021

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Fasinjoji Biyu Sun Mutu Sakamakon Ruftawar Gada A Ebonyi

Published

on

Rundunar ƴan sanda a jihar Ebonyi sun tabbatar da mutuwar wasu fasinjoji biyu sanadin ruftawar wata gada a jihar.

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Joshua Ukandu ne ya tabbatar da haka a Abakaliki yau Litinin.

Ya ce lamarin ya faru da misakin ƙarfe 10:00am na safiyar yau a ƙauyen Mgbabeluzor da ke ƙaramar hukumar Izzi a jihar.

Ya ce tuni aka kai gawar mutanen babban asibitin Iboko sashen ajiye gawarwaki.

Gadar wadda ake gyaranta ta rufta yayin da ma’aikatan ke kusa da ita.

Sannan mutanen biyu sun mutu ne sakamakon munanan rauni da su ka samu.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Edo Ya Amince Da Dubu 70 Matsayin Mafi Karancin Albashi

Published

on

Gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki ya amince da dara biyan ma’aikatan jihar mafi ƙarancin albashi naira 70,000.

Obaseki ya bayyana haka yau Litinin yayin ƙaddamar da gidan ma’aikata.

Ya ce zai fara biyan mafi karancin albashin daga watan Mayu mai kamawa.

Batun ƙarin albashi na daga cikin dalilai da ya sa kungiyoyin kwadago a Najeriya ke yin zanga-zanga wanda su ka buƙaci a ƙarawa ma’aikata a kowanne mataki.

A baya ƙungiyar ta bukaci a mayar da mafi ƙarancin albashin naira 30,000, sai sai sun bukaci ƙari bayan da aka cire tallafin mai a shekarar 2023.

Sai dai wasu gwamnonin sun nuna ƙin amincewa da haka a baya.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Kotu Ta Sanya Ranar Da Za Ta Yankewa Ganduje Hukunci Kan Zargin Rashawa

Published

on

Babbar kotun jihar Kano ta tsayar da ranar yanke hukunci dangane da zargin tsohon gwamnan jihar Abdullahi Ganduje bisa karɓar rashawa.

 

Kotun ƙarƙashin mai shari’a Usman Malam Na’abba, ta tsayar da ranar 16 ga watan Mayu a matsayin ranar da za ta yanke hukuncin bayan sauraron kowanne bangare.

 

An shigar da ƙarar tsohon gwamnan Kano Abdullahi Ganduje da matasar da ɗansa kan zargi takwas wanda ciki akwai cin hanci, karkatar da kudaɗe da sauransu.

 

Baya ga tsohon gwaman, akwai wani kamfani da aka shigar da ƙarar wanda yana daga cikin waɗanda ake ƙara.

 

Gwamnatin Kano ce ta gurfanar da su a gaban kotu, tare da gabatarwa da kotu shaidu 15 a kan zargin da take musu.

 

Bayan sauraron ɓangaren masu ƙara da waɗanda ake ƙara, kotun ta tsayar da ranar 16 ga watan Mayu domin yanke hukunci a kai.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: